Aminiya:
2025-07-06@02:49:54 GMT

Kada ku karaya da shigo da abinci daga ƙasar waje — IAR

Published: 4th, May 2025 GMT

Cibiyar Binciken Aikin Gona ta Jami’ar Ahmadu Bello da ke Samaru Zariya ta hori manoma da kada su yi fargaba bisa yadda Gwamnatin Tarayya ke shigo da abinci daga ƙasashen waje.

Shugaban Cibiyar, Farfesa Ado Yusuf ya ba da shawarar ce a yayin zantawa da manema labarai jim kaɗan bayan kammala taron bita da tsare-tsaren aikin noma na shekarar 2025 da ya gudana a dakin taro na Tanimu Balarabe da ke Cibiyar IAR Samaru, Zaria.

Abin da ya hana ni cika alƙawarin da na yi wa ma’aikata — Gwamnan Sakkwato Lakurawa sun kashe ’yan bijilanti 11 a Sakkwato

Ya tunasar da manoma cewa, nau’o’in abincin da suke nomawa ba a kasar nan kadai ake amfani da su ba, don haka kayan amfanin gonarsu zai ci gaba da daraja a wasu sassa na kasashe duniya da suke neman su.

Farfesa Yusuf ya kara da cewa, har yanzu abubuwan da ake nomawa a kasar nan ba ya wadatar da bukatun ‘yan kasa ballantana a rasa yadda za a siyar da su.

Sai dai kuma shugaban cibiyar ya yi kira da a dauki matakan da suka dace wajen kayyade irin kayan abincin da ake shigowa da su don cim ma burin da ya sa gwamnati ta dauki matakin.

Masanin aikin gonar daga nan sai ya shawarci Gwamnatin Tarayya da ta wadata manoma da muhimman kayan aikin noma, domin ci gaba da ba su ƙwarin gwiwar aikin gona, domin kada shigowa da kayan abincin ya karya masu gwiwa.

Ya tabbatar da cewa, duk da kokarin gwamnati na shigowa da abinci daga waje, wanda ya karya farashin kayan abinci, manoma sun sami ribar noma daidai gwargwado a daminar bara.

Farfesa Yusuf ya ƙara da cewa, “ina cikin masu son ganin manoma sun sami ribar noma, amma kuma ba na son ganin an tsawwalawa wa jama’a ta inda farashin kayan abinci zai hana talaka sayen abin da zai ci.”

Shugaban Cibiyar IAR ya kara da cewa, duk da Nijeriya na shigowa da kayan abinci, har yanzu ana kuma safarar kayan gona zuwa wasu ƙasashen waje, don haka ya jaddada buƙatar da ke akwai ta samar da ingantattun kayan aikin noma kuma cikin farashi mai rahusa da manoma za su iya mallaka.

Ya bayyana cewa, hauhawar farashi da tsadar kayan noma na iya hana manoma noma isasshen abinci ga kasa, wanda haka zai iya sanadin durkushewar mafi yawa daga cikinsu kuma ya sa su watsar da aikin gona.

Don haka ya roƙi gwamnatin da ta gaggauta ɗaukar matakan sauƙaƙa wa manoma da ribanya ƙwazonsu da wadata ƙasa da abinci.

Da yake tsokaci dangane da ayyukan cibiyar, Farfesa Yusuf ya ce, a wannan shekara ta 2025, cibiyar za ta gudanar da ayyukan bincike a kan aikin noma har sama da guda 180, yayin da za ta bai wa wasu aikace-aikacen gona 32 muhimmanci don bai wa manoma ingantattun dabaru tare da sauke nauyin da ke kan cibiyar na habaka aikin noma a kasa.

Tun farko da yake nasa jawabin, shugaban taron kuma Shugaban Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, Farfesa Kabir Bala ya ce, duk da dai yana halartar taron ne a karo na karshe a matsayinsa na shugaban jami’ar duk da haka cibiyar za ta ci gaba da samun dukkan taimako da kwarin gwiwar da take bukata daga gare shi.

Farfesa Bala wanda ya nuna jin dadinsa bisa yadda aka tattara masana aikin gona daga jihohi daban-daban na kasar nan, inda ya yi fatan za a fito da wata matsaya da za a habaka samar da abinci da kuma saukaka wa ‘yan kasa yadda za su same shi cikin sauki kuma a wadace.

Sai dai kuma ya roki gwamnati da ta samar da karin kudade ga cibiyar don ci gaba da gudanar da ayyukan binciken sababbin dabarun aikin gona.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: IAR kayan abinci

এছাড়াও পড়ুন:

Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace

Kazalika, gazawar Hukumar Bayar Da Agajin Gaggawa ta Kasa NEMA da kuma sauran hukumomin na jihohi na sauke nauyinsu, hakan ya nuna a zahiri, na irin kalubalen da ake fuskanta, na rashin sauke nauyinsu, na bayar da agajin na gaggawa.

Misalii, an ruwaito cewa, a sansanin na ‘yan gudun hijira na Yelwata, musamman yadda suke kwana a kan tandarmin kasa, tare da kokawa da cizon Sauro, ‘ya’yansu ke ci gaba da zama a cikin yunwa, wanda hakan, ya kara harzuka su, fita yin zanga-zangar.

Bisa wasu akaluma da aka samu daga Biniwe, sun nuna cewa, a sansanin na Yelwata, an samu haihuwa 15 da kuma mata da suka samu juna biyu, su 122, wadanda kuma suke ci gaba da rashin samun kulawar kiwon lafiyarsu, hakan kuma ya jefa, rayuwar jariransu, a cikin hadari.

Bugu da kari, a sansanin ‘yan gudun hijira na jihar Nasarawa, an samu kwararowar sama da ‘yan gudun hijira guda 4,000 daga sansanin ‘yan gudun hijira na Biniwe.

Wannan ya zama wani babban nauyin wajen ciyar da su da kuma rashin samar masu da wajen wadatattun wajen kwana da rashin tsafta.

Kusan a daukacin sansanonin ‘yan gudun hijira, kamar na jihohin Borno da Adamawa, dubban ‘yan gudun hijirar da yaki da ‘yan ta’addar Boko Haram ya tarwatsa su daga matsugunan su, suna ci gaba da fuskantar karancin ruwan sha, magunguna, inda kuma ake samun barkewar Kwalara, wanda hakan, ke janyo rasa rayukan wadanda lamarin ya rutsa da su.

Wadannan misalan kadai, sun nuna irin rashin gazawar kula da yanayin da bil’Adama ke ciki.

Hukumar NEMA, wadda aka dora mata nauyin bayar da dauki kan aukuwar annoba, ta gaza sauke wannan nayin nata.

Sai dai, har yanzu zamu ci gaba da yin magana domin NEMA ta sauke nauyin da aka dora mata, musamman na bayar da agajin na gaggawa ga wadanda wani iftila’i, ya fada masu.

Kazalika, kayan agajin da Hukumar ta tura zuwa sansani na Yelwata, bayan kai hare-haren a yankin, idan aka yi dubi da lokacin da aka kai kayan da rashin kai wadatattunsu, wannan babban abin tambaya ne da har yanzu, ke bukatar amsa, musamman, kan yadda aka zargin wasu jami’an na NEMA, na karkatar da kayan na agajin.

Bugu da kari, hakan ya nuna irin yadda a 2024, NEMA ta fuskanci suka da zargi, na boye kayan da ya kamata a rabawa ‘yan gudun hijira a dakunanta na adana kayan agaji, wanda hakan ya jefa rayuwar ‘yan gudun hijira, musamman wadanda ke a Arewa Masu Gabas, a cikin kuncin rayuwa.

A dai jihar ta Biniwe, Hukumar Bayar Da Agajin Gaggawa ta jihar SEMA, ta fuskanci suka kan yin watsi da ‘yan gudun hijira na Yelwata, musamman duba da yadda aka barsu, a cikin kangin yunwa, cizon Sauro, wanda kuma aka yi zargin, wasu jami’an na SEMA, sun karkatar da kayan agajin, da ya kamata a raba masu.

Hakan ma batun ma yake a jihar Adamawa, inda aka zargi Hukumar SEMA ta jihar, kan kin rabar masu da kayan dauki kan lokaci, wanda hakan ya haifar da zanga-zanga a watan Mayun 2025.

Sai dai, wadanan Hukumomin suna bugewa da dora laifin kan rashin ba su kudaden da ya kamata Gwamnatin Tarayya ta tura masu.

Hakazalika, rashin taka rawar da ya kamata ‘yan majalisu da matakan gwamnati ya kamata su yi, na rabar da kayan dauki ga alumma, hakan ya kara kawo rudani, kan batun na bayar da daukin.

Shirye-shiryen rabar da kayan tallafin rage radadin kuncin rayuwa, hakan ya sanya an fifita mazauna birane da ‘yan lelen ‘yan siyasa, inda su kuma ‘yan gudun hijira, aka mayar da su, saniyar ware.

A jihar ta Biniwe duk da kudaden da gwamnatin jihar kebewa da kananan hukumomin jihar da kuma wanda take kebewa sarakunan gargajiya, amma abin bakin cikin shi ne, ba kebe kudaden, da ya kamata a tallafawa ‘yan gudun hijira na jihar, inda gwamnatin ke fakewa, da cewa, tana fuskantar karancin kudade.

Karkatar da kayan agajin da ya kamata a kai wa ‘yan gudun hijirar na Yelwata, hakan ya nuna cewa, ba a dauki rayuwarsu, da wata mahimmanci ba.

Bisa ra’ayin wannan Jaridar, ya zama wajibi zababbun ‘yan majalisar kasar, su mayar da hankali wajen fifita kula da rayuwar ‘yan gudun hijira, musamman ta hanyar kebe masu wani gwa-gwaban kaso a cikin kasafin kudi na kasar da kuma kirkiro da dokokin da za su tabbatar da an yi adalci, wajen rabar masu da kayan tallafi da kuma daukar kwakwaran hukunci, ga duk wanda ya karkatar da kayan tallafin da aka yi niyyar kai masu.

Bugu da kari, ya zama wajbi matakan gwamnati uku na kasar da su kebe kudade da za a rinka taimaka wa ‘yan gudun hijira kai tsaye da ke a sansanonin su da samar masu da abinci, da kayan kula da lafiyarsu da wajen kwana da kuma sanya ido kan kayan domin a dakile yin cuwa-cuwa da kayan.

Ya zama wajbi kananan hukumomi da masarautu da gwamnatin jihohi ke tallafa masu da kudaden gudanar da ayyukansu, su yi hadaka da jagororin alummomi domin su gano tare da ganin ana tallafa wa ‘yan gudun hijirar, yadda ya dace.

Hakazalika, ya zama wajibi, a yiwa hukumomin NEMA da SEMA garanbawul, musamman domin a dawo da ainahin kimarsu, yadda ya kamata.

Zanga-zangar ta ‘yan gudun hijirar na Yelwata, wata ‘yar manuniya ce, da ke nuni da cewa, ya zama wajbi, a dauki matakan da suka wajaba, na irin halin da suke ciki.

Duba da cewa, a Nijeriya akwai ‘yan gudun hijira da yawansu ya kai sama da miliyan uku, hakan ya nuna cewa, ba wai kawai alkarin baki ya suka cancanta ba, amma kula da rayuwarsu, yadda ta kama, shi ne mafita.

Kazalika, duba da cewa, ana cikin yanayi na damina a kasar, akwai kuma wani karin barazanar da ke tafe, mai yuwa za a iya samun ambaliyar rayuwan sama wanda hakan zai janyo tarwatsa alumomi daga matsugunasu, inda hakan ya nuna cewa, tun yanzu, ya zama waji, a dauki matakan gaggawa.

Ya kamata ‘yan majalisa da shugabannin kananan hukomin da sarakunan gargajiya, su nuna cewa, da gaske suke wajen jin kan rayuwar ‘yan gudun hijira, sama da na su kudurorin na kashin kansu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  IRGC: Duk Wani Wuce Gona Da Iri Na ‘Yan Sahayoniya Zai Gaggauta Rushewarsu
  • Tsadar rayuwa ta sa ’yan Nijeriya na siyan abincin da ya lalace
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci
  • Ana Tuhumar Tsohon Ɗan Wasan Arsenal Thomas Partey Da Laifin Fyaɗe A Ƙasar Ingila
  • Ayyukan ‘Yan Ta’adda Na Barazana Ga Shirin Gwamnati Na Wadata Kasa Da Abinci
  • Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Harin Kan Cibiyar Makamashin Nukiliya Cin Amanar Diflomasiyya Ce
  • Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal
  • Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 50 A Benue
  • Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram