Aminiya:
2025-09-18@02:19:04 GMT

Ya kamata a zuba jari a harkar noman rani — Zulum

Published: 4th, May 2025 GMT

Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara ya bukaci Hukumar Raya Yankin Tafkin Chadi (CBDA) da ta sanya hannunjari sosai a fannin noman rani a kewayen yankin Tafkin Chadi, domin bunkasa wadatar abinci da kuma farfado da tattalin arziki a fadin jihar da kuma yankin Arewa maso Gabas.

Gwamna Zulum ya yi wannan kiran ne a lokacin da shugaban hukumar Farfesa Abdu Dauda Biu ya kai masa ziyarar ban girma a gidan gwamnati da ke Maiduguri.

Wa zai cire wa Real Madrid kitse a wuta? Mai shekara 92 ya shiga gasar Gudun Fanfalaƙi karo na 30 a jere

Da yake karin haske kan yadda ake noma a yankin, gwamnan ya bayyana cewa, gabar Tafkin Chadi, musamman yankunan da suka hada da Kirenowa da Marte da Gamborun Ngala da Baga suna da albarkatu masu yawa na ruwan karkashin kasa da kuma filayen noma da ya dace da noman rani.

“Ina so in ja hankalinku game da kasancewar ruwan kasa mai yawa a gabar Tafkin Chadi. Kada mu dogara ga ruwa sama kawai,” in ji Zulum.

Ya kara da cewa, “kwanan nan na aika da tawagar bincike don gano gaskiya zuwa Gamborun Ngala, kuma tawagar ta tabbatar mana da samun albarkatun ruwan karkashin kasa, wadanda za mu iya amfani da su wajen noman rani ta hanyar ban-ruwa.”

Gwamna Zulum ya kuma bayyana cewa, gwamnatin jihar ta ba da kimanin Naira biliyan 2 domin noma hekta 1,000 na gonaki ta hanyar amfani da na’urar noman rani mai amfani da hasken rana a garin Baga.

Sannan an ware ƙarin Naira biliyan 1.5 domin gudanar da irin wadannan ayyuka a garuruwan Gamborun Ngala da Marte, wadanda dukkansu ke gab da kammaluwa.

“A kokarinmu na farfado da shirin noman rani na a Gabar Tafkin Chadi ta Kudu, a halin yanzu muna noman fili mai fadin hekta 1,000 a karkashin aikin noman rani na Baga a kan kudi kimanin Naira biliyan 2.

Bugu da kari, muna samar da hekta 200,000 a Gamboru da kuma wata hekta 200,000 na samar da wutar lantarki ta Lamboru ta hanyar amfani da tsarin ban-ruwa, don farfado da ayyukan noma a fadin yankin,” in ji zulum.

Farfesa Zulum ya ci gaba da cewa, gwamnatinsa ta yi nasarar haka rijiyoyi kusan 3,000 a Damasak da ke Karamar Hukumar Mobbar, wanda hakan ya bai wa manoma damar yin noma a fili mai tsawon kilomita 16, matakin da ya bullo da hanyar noman ruwan karkashin kasa a yankin da a baya ba a saba da yin irin sa ba.

Gwamnan ya yi alkawarin ci gaba da hada kai da hukumar CBDA, domin fadada noman a Ngala da Damasak da New Marte da samar da ababen more rayuwa ga wadanda suka dawo da kuma tabbatar da dorewar samuwar abinci.

Ya kuma bayyana aniyar gwamnatin jihar na tallafawa wajen farfado da Tashar Famfunan Ruwa ta Chadi Basin Kirenowa, inda ya ce ana kokarin kafa bataliyar soji a yankin domin inganta tsaro.

“A matsayinmu na gwamnati, za mu so sanin inda za mu iya shiga saboda abubuwan da za a iya samu suna nan. Ina tuntubar Shugaban kasa da shugabannin sojoji kan yiwuwar kafa bataliyar soji a Kirenowa da nufin kare tashar famfon,” in ji Zulum.

A nasu jawabin shugaban hukumar Farfesa Abdu Dauda Biu da Manajin Darakta, Alhaji Tijjani Tumsa sun sanar da gwamnan cewa, an kafa sabuwar hukumar ce a ranar 13 ga watan Disamba 2024.

Sun bayyana cewa, sun ziyarci muhimman wurare da ke karkashin kulawarsu, ciki har da Madatsar Ruwa ta Alau, sun kuma yaba wa Gwamna Zulum kan yadda yake gudanar da ayyukanta.

Shugabancin Hukumar ta CBDA ya yi alkawarin hada kai da gwamnatin jiha don aiwatar da ayyukan da suka shafi noman rani da kiwon dabbobi da kamun kifi.

Sun kuma nemi goyon bayan gwamnan don ganin an kammala gyaran madatsar ruwa ta Alau a kan lokaci, wanda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince da shi a kwanakin baya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Babagana Umara Zulum Noman rani

এছাড়াও পড়ুন:

Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar

Wasannin Duniya Ba

Fira ministan kasar ta Spain ya bayyana hakan ne dai a yayin da yake nuna jin dadinsa danagen da gagarumar Muzaharar da mutanen kasar su ka yi ta nuna kin amincewarsu da shigar kasar ta Yahudawa cikin tseren kekune.

Fira ministan kasar ta Spain Pedro Sánchez Pérez ya ce: ” Har zuwa lokacin da za a kawo karshen kisan kiyashi a Gaza, bai kamata a kyale Isra’ila ta rika shiga cikin gasar wasannin kasa da kas aba.

A yau litinin ne dai Fira ministan kasar ta Spain ya gabatar da jawabi gabanin taron ‘yan majalisa masu wakiltar jam’iyyun gurguzu, ya yi ishara da taho mu gamar da aka yi a tsakanin masu kin jinin kisan kiyashin da HKI take yi wa Falasdinawa da masu goyon bayanta, sannan ya kara da cewa; a kodayaushe ba mu aminta da tashin hankali ba.

Mutane 20 ne dai su ka jikkata a yayin wannan taho mu gama din a babban birnin kasar ta Spain,Madrid.

Fira ministan Pedro Sánchez Pérez   ya kuma yi wa hukumomin wasanni na duniya tamabya da cewa; Me ya sa aka haramtawa Rasha shiga cikin wasannin kasa da kasa saboda yakin Ukiraniya,amma ba a kori Isra’ila ba?.

Al’ummar kasar Spain da mahukuntanta suna cikin nag aba-gaba a cikin nahiyar turai wajen nuna kin amincewa da yi wa mutanen Gaza kisan kiyashi.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha September 15, 2025  Dan Kasar Iran Mai Kirkira Ya Sami Kyautar Yabo A Kasar China September 15, 2025 Fizishkiyan:  Wajibi Ne Musulmi Su Hada Kai Domin Dakatar Da Laifukan HKI September 15, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha September 15, 2025 Kwamitin Kolin Tsron Kasar Iran Ya Amince Da Yarjejeniyar Da Aka Cimma Da Hukumar IAEA September 15, 2025 Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar September 15, 2025 Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000 September 15, 2025 Gwamnatin Sudan Ta Ce: Babu Sulhu Da ‘Yan Tawayen Kasar Na Kungiyar Rapid Support Forces September 15, 2025 Kasashen Larabawa da na Musulmi na taron gaggawa kan harin Isra’ila a Qatar September 15, 2025 Hamas ta bukaci kasashen musulmi da na Larabawa su dauki mataki mai tsari kan Isra’ila September 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Chadi:  Majalisa ta amince a baiwa shugaban kasa  damar ci gaba da Mulki har karshen rayuwa
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
  • Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari
  • Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila
  • Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya tare da kiyaye hadin kai
  • Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”
  • Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar