Ya kamata a zuba jari a harkar noman rani — Zulum
Published: 4th, May 2025 GMT
Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara ya bukaci Hukumar Raya Yankin Tafkin Chadi (CBDA) da ta sanya hannunjari sosai a fannin noman rani a kewayen yankin Tafkin Chadi, domin bunkasa wadatar abinci da kuma farfado da tattalin arziki a fadin jihar da kuma yankin Arewa maso Gabas.
Gwamna Zulum ya yi wannan kiran ne a lokacin da shugaban hukumar Farfesa Abdu Dauda Biu ya kai masa ziyarar ban girma a gidan gwamnati da ke Maiduguri.
Da yake karin haske kan yadda ake noma a yankin, gwamnan ya bayyana cewa, gabar Tafkin Chadi, musamman yankunan da suka hada da Kirenowa da Marte da Gamborun Ngala da Baga suna da albarkatu masu yawa na ruwan karkashin kasa da kuma filayen noma da ya dace da noman rani.
“Ina so in ja hankalinku game da kasancewar ruwan kasa mai yawa a gabar Tafkin Chadi. Kada mu dogara ga ruwa sama kawai,” in ji Zulum.
Ya kara da cewa, “kwanan nan na aika da tawagar bincike don gano gaskiya zuwa Gamborun Ngala, kuma tawagar ta tabbatar mana da samun albarkatun ruwan karkashin kasa, wadanda za mu iya amfani da su wajen noman rani ta hanyar ban-ruwa.”
Gwamna Zulum ya kuma bayyana cewa, gwamnatin jihar ta ba da kimanin Naira biliyan 2 domin noma hekta 1,000 na gonaki ta hanyar amfani da na’urar noman rani mai amfani da hasken rana a garin Baga.
Sannan an ware ƙarin Naira biliyan 1.5 domin gudanar da irin wadannan ayyuka a garuruwan Gamborun Ngala da Marte, wadanda dukkansu ke gab da kammaluwa.
“A kokarinmu na farfado da shirin noman rani na a Gabar Tafkin Chadi ta Kudu, a halin yanzu muna noman fili mai fadin hekta 1,000 a karkashin aikin noman rani na Baga a kan kudi kimanin Naira biliyan 2.
Bugu da kari, muna samar da hekta 200,000 a Gamboru da kuma wata hekta 200,000 na samar da wutar lantarki ta Lamboru ta hanyar amfani da tsarin ban-ruwa, don farfado da ayyukan noma a fadin yankin,” in ji zulum.
Farfesa Zulum ya ci gaba da cewa, gwamnatinsa ta yi nasarar haka rijiyoyi kusan 3,000 a Damasak da ke Karamar Hukumar Mobbar, wanda hakan ya bai wa manoma damar yin noma a fili mai tsawon kilomita 16, matakin da ya bullo da hanyar noman ruwan karkashin kasa a yankin da a baya ba a saba da yin irin sa ba.
Gwamnan ya yi alkawarin ci gaba da hada kai da hukumar CBDA, domin fadada noman a Ngala da Damasak da New Marte da samar da ababen more rayuwa ga wadanda suka dawo da kuma tabbatar da dorewar samuwar abinci.
Ya kuma bayyana aniyar gwamnatin jihar na tallafawa wajen farfado da Tashar Famfunan Ruwa ta Chadi Basin Kirenowa, inda ya ce ana kokarin kafa bataliyar soji a yankin domin inganta tsaro.
“A matsayinmu na gwamnati, za mu so sanin inda za mu iya shiga saboda abubuwan da za a iya samu suna nan. Ina tuntubar Shugaban kasa da shugabannin sojoji kan yiwuwar kafa bataliyar soji a Kirenowa da nufin kare tashar famfon,” in ji Zulum.
A nasu jawabin shugaban hukumar Farfesa Abdu Dauda Biu da Manajin Darakta, Alhaji Tijjani Tumsa sun sanar da gwamnan cewa, an kafa sabuwar hukumar ce a ranar 13 ga watan Disamba 2024.
Sun bayyana cewa, sun ziyarci muhimman wurare da ke karkashin kulawarsu, ciki har da Madatsar Ruwa ta Alau, sun kuma yaba wa Gwamna Zulum kan yadda yake gudanar da ayyukanta.
Shugabancin Hukumar ta CBDA ya yi alkawarin hada kai da gwamnatin jiha don aiwatar da ayyukan da suka shafi noman rani da kiwon dabbobi da kamun kifi.
Sun kuma nemi goyon bayan gwamnan don ganin an kammala gyaran madatsar ruwa ta Alau a kan lokaci, wanda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince da shi a kwanakin baya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Babagana Umara Zulum Noman rani
এছাড়াও পড়ুন:
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba
Sai dai don neman cimma burinta na “sake mayar da kasar Amurka zakaran gwajin dafi”, kasar Amurka ta sha daukar matakai na dakile ci gaban kasar Sin, ciki har da katse huldar tattalin arziki da ita da ma sanya takunkumai ga kamfanoninta masu ci gaban kimiyya da sauransu, duk da hakan, kasar Sin ta kiyaye bunkasar tattalin arzikinta yadda ya kamata, har ma karuwar tattalin arzikinta ta kai kaso 5.2% a cikin watanni tara na farkon bana, lamarin da ya shaida inganci da juriya na tattalin arzikin kasar. A kwanan nan, kasar Sin ta zartas da shawarwarin da aka gabatar game da tsara shirin raya tattalin arziki da zaman al’umma cikin shekaru biyar masu zuwa, kuma bisa ga shawarwarin, za a tsara shirin raya kasa na shekaru biyar biyar karo na 15 na kasar. Cikin sama da shekaru 70 da suka wuce, kasar Sin ta yi ta kokarin aiwatar da shirye-shiryen ba tare da kasala ba, ba don neman kalubalantar wata ko maye gurbinta ba, amma don mai da hankali a kan raya kanta da kuma bayar da damammaki na samun ci gaba ga sauran kasashen duniya.
Ganawar da aka yi a wannan karo ta kasance ta farko a tsakanin shugabannin kasashen biyu tun bayan da shugaba Trump ya sake hawa karagar mulkin kasar Amurka. Kafin wannan kuma, shugabannin biyu sun taba tattaunawa da juna ta wayar tarho har sau uku, don nuna alkiblar bunkasar huldar kasashensu. Tun bayan watan Mayun da ya gabata, bisa daidaiton da shugabannin biyu suka cimma, tawagogin kasashen biyu sun gudanar da shawarwarin tattalin arziki da cinikayya har sau biyar. A sabon zagayen shawarwarin da aka gudanar a baya bayan nan a birnin Kuala Lumpur, sassan biyu sun yi musayar ra’ayoyi kan batutuwan tattalin arziki da ciniki da ke janyo hankulansu duka, tare da cimma matsaya daya a kan matakan da za a dauka. Lallai ta hanyar yin shawarwari da juna cikin daidaito, sassan biyu sun kai ga karfafa fahimtar juna da amincewa da juna, hakan kuma ya shaida cewa, yin shawarwari da juna ya fi yin gaba da juna, kuma Sin da Amurka suna iya raya kansu tare da tabbatar da ci gabansu na bai daya.
Kasancewarsu kasashe biyu mafiya karfin tattalin arziki a duniya, alhakin da ke rataya a wuyan Sin da Amurka ne su gano hanyar da ta dace ta cudanya da juna. Kasashen biyu za su iya karfafa ginshikin huldarsu da samar da kyakkyawan yanayi na bunkasa kansu, tare da samar da karin tabbas da kwarin gwiwa ga duniya, muddin sun tabbatar da daidaiton da shugabanninsu suka cimma, kuma suka yi hangen nesa tare da nacewa ga yin shawarwari da juna wajen daidaita sabaninsu, da kuma inganta hadin gwiwarsu da mu’amala da juna a kai a kai.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA