An Share Filin Noma Kadada 100 Don Karfafa Matasa Su Yi Noma A Babura Jihar Jigawa
Published: 4th, May 2025 GMT
Shugaban karamar hukumar Babura ta jihar Jigawa, Malam Hamisu Muhammad Garu, ya kaddamar da shirin karfafa aikin gona da nufin sanya matasa aikin noman shinkafa a wani bangare na kokarin inganta ayyukan yi da samar da abinci a yankin.
Da yake jawabi yayin bikin kaddamar da aikin aka gudanar a garin Babura, shugaban ya bayyana cewa, Gwamna Malam Umar Namadi ne ya bullo da shirin a matsayin wani muhimmin mataki na samar da guraben ayyukan yi ga matasa, da habaka tattalin arzikin kananan hukumomi, da karfafa samar da abinci a fadin jihar.
A cewarsa, gwamnatin jihar ta samar da muhimman kayayyakin amfanin gona da suka hada da takin zamani, magungunan kashe kwari, irin shinkafa mai yawan gaske, da injinan feshi.
Malam Hamisu Garu ya yi nuni da cewa, za a raba kayayyakin ga matasa 200 da aka zabo daga sassa daban-daban na karamar hukumar.
Ya kara da cewa, karamar hukumar ta ware tare da share fili mai fadin hekta 100 domin fara aikin.
Shugaban ya nuna jin dadinsa ga gwamnatin jihar da ta fara shirin.
Ya ce, shirin zai hana matasa yin kaura zuwa birane domin neman ayyukan yi, lamarin da yakan jefa su cikin hatsari da kuma gurgunta makomarsu.
A nasa jawabin, babban daraktan cibiyar bincike ta jiha Dakta Suleman Rufa’i, ya bayyana shirin a matsayin wani kokari na farko, inda ya kara da cewa akwai shirye-shiryen kara fadada shi bisa burin gwamnati na mayar da jihar Jigawa a matsayin jihar da ke kan gaba wajen samar da abinci a Nijeriya.
Rediyon Nijeriya ya ruwaito cewa, sarakunan gargajiya da suka halarci taron sun hada da Hakimin Babura, Sarkin Ban Ringim, Alhaji Muhammad Nata’ala Mustapha, da Hakimin Garu, Dan-makwayon Ringim, Alhaji Suhailu Abubakar Usman, sun yabawa gwamnati kan wannan shiri.
Shugabannin sun bukaci wadanda suka ci gajiyar shirin su nuna kishin kasa da alhaki ta hanyar amfani da tallafin yadda ya kamata domin tabbatar da nasarar shirin.
USMAN MZ/Dutse
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Sha Alwashin Inganta Kwazon Kananan Hukumomin Jihar
Majalisar Dokokin Jihar Jigawa ta jaddada kudurin ta na bada managartan shawarwari da za su yi wa kananan hukumomin jihar jagoranci wajen gudanar da ayyukan su kamar yadda yakamata.
Shugaban Kwamatin Kananan Hukumomi na Majalisar, Alhaji Aminu Zakari, ya bada wannan tabbacin lokacin rangadin kwamatin majalisar a sakatariyar karamar hukumar Birniwa.
Alhaji Aminu Zakari Wanda shi ne wakilin mazabar Gwiwa, yace ziyarar Kwamatin na daga nauyin da aka dorawa bangaren majalisa wajen bibiyar yadda Gwamnati ta ke aiwatar da manufofi da shirye shirye domin tabbatar da shugabanci nagari.
Alhaji Aminu Zakari yace haka kuma Kwamatin yana la’akari da batun zamantakewar jama’ar da tattalin arziki a matsayin ma’aunin ci gaban rayuwa da koma bayana domin baiwa bangaren zartaswa shawarwari dan bullo da manufofi da shirye shiryen da za su dace da bukatun Jama’a.
Yace , ziyarar na bada damar ganawa da bangaren zartaswa da na kansiloli da ma’aikata domin tabbatar da tsarin aiki tare ta hanyar kyakkyawar fahimtar juna.
A daya bangaren kuma, kananan kwamitocin da Babban Kwamatin kananan hukumomi na majalisar dokokin jihar Jigawan ya kafa, sun sami nasarar tantance ayyukan raya kasa da karamar hukumar Birniwa ta gudanar a sassan yankin daga watan Oktobar 2024 kawo yanzu.
Karamin Kwamati na daya, bisa jagorancin wakilin mazabar Alhaji Muhammad Abubakar Sa’id ya duba aikin Masallacin kamsissalawati na Kakori, da gyaran masallacin juma’a na Malandi, da sanya fitilu masu amfani da hasken rana a Taljari da shaguna da rumfuna a kasuwar Birniwa da wasu muhimman wurare da suka hada da gyaran gidajen karamar hukumar da gyaran kotun shari’a a Birniwa.
Karamin Kwamati na biyu bisa jagorancin wakilin mazabar Guri, Alhaji Usman Abdullahi Tura Musari, ya duba aikin gina shago guda biyar a bakin Babban titin garin Birniwa da shaguna da rumfuna da cikon kasa a garin Kupsa da masallacin kamsissalawati a kauyen Garuba.
Kazalika, ziyarar Kwamatin ta duba batun daukar malaman duba gari 22 da Gina ajujuwa a makarantun ‘Yayan fulani.
Tunda farko, shugaban karamar hukumar Birniwa, Malam Shehu Baba Birniwa, ya bayyana aniyarsa ta aiki da shawarwarin Kwamatin domin cigaban karamar hukumar sa.
Malam Shehu Baba ya ce tun daga kama mulkinsa ya bar kofar sa a bude da nufin cusa dabi’ar aiki tare da masu ruwa da tsaki a matsayin turba mai sauki wajen gudanar da mulkin karamar hukumar.
Usman Mohammed Zaria