Iragchi Ya Zanta Ta Wayar Tarho Da Babban Sakataren MDD Antonio Guterres
Published: 4th, May 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Argchi ya zanta ta wayar tarho da babban sakataren MDD Antonio Guterres inda ya fada masa inda aka kwana a tattaunawar da kasarsa take da Amurka ba kai tsaye ba.
Kamfanin dillancin labaran Ip na kasar Iran ya nakalto Arigchi yana fadawa babban sakatarin kan cewa akwai bukatar bangarorin biyu su yi gaske don cimma yarjeniya wacce kowa ya amince da ita.
Tattaunawar dai tana nuna irin yadda Iran ta fifita tattaunawa da kuma hanayr diblomasiyya kan shiga wasu rigingimu wadanda basa da amfani.
Aragchi ya fadawa Goterres kan cewa Iran tana bukatar ta ci gaba shirinta na makamashin nukliya ta zaman lafiya. Sannan a dauke mata takunkuman zaluncin da aka daura mata.
Ya kuma kara da cewa Iran tana daga cikin kasashen da suka sanya hannu a yarjeniyar NPT wacce ta bata samar amfanin da makamacin nukliya ta zaman lafiya. Banda haka irana tana son ta shiga tattaunawa da kasashen Turai don warware matsalar shirin makamashin nukliya ta kasar ba tare da an harba harsashi go guda ba.
Ana bangare babban sakataren MDD ya yaba da tunanin tattaunawa ba kai tsaye ba , sannan ya taya kasar bakin ciki kan gobarara da ta tashi a tashar jiragen ruwa ta Ali Ra’ei a bandar Abbas.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An garzaya da ’yan Isra’ila 154 asibiti bayan harin Iran
Isra’ila ta tabbatar cewa an garzaya da ’yan ƙasarta aƙalla 154 asibiti bayan sabbin hare-haren ramuwar gayya da Iran ta kawo mata.
Ma’aikatar lafiyar Isra’ila ta ce aƙalla mutum huɗu daga cikin waɗanda aka kai asibitin suna cikin halin rai-kwakwai-mutu-kwakwai, wasu biyar kuma na samun kulawa ta musamman saboda tsananin tashin hankali.
Alkaluman da ma’aikatar ta fitar sun nuna cewa mutum 130 daga cikin majinyatan sun samu raunuka marasa tsanani a sakamakon hare-haren.
Wannnan na zuwa ne a yayin da Iran ta ci gaba luguden rokoki a matsayin ramuwar gayya a sassan Isra’ila a a ranar Talata.
Isra’ila ta ce Iran ta lashe mata mutane akalla 24.
A ɗaya ɓangaren kuma Iran cewa harin tsokana da Isra’ila ta kai mata ya yi ajalin kimanin mutum 224.