Iragchi Ya Zanta Ta Wayar Tarho Da Babban Sakataren MDD Antonio Guterres
Published: 4th, May 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Argchi ya zanta ta wayar tarho da babban sakataren MDD Antonio Guterres inda ya fada masa inda aka kwana a tattaunawar da kasarsa take da Amurka ba kai tsaye ba.
Kamfanin dillancin labaran Ip na kasar Iran ya nakalto Arigchi yana fadawa babban sakatarin kan cewa akwai bukatar bangarorin biyu su yi gaske don cimma yarjeniya wacce kowa ya amince da ita.
Tattaunawar dai tana nuna irin yadda Iran ta fifita tattaunawa da kuma hanayr diblomasiyya kan shiga wasu rigingimu wadanda basa da amfani.
Aragchi ya fadawa Goterres kan cewa Iran tana bukatar ta ci gaba shirinta na makamashin nukliya ta zaman lafiya. Sannan a dauke mata takunkuman zaluncin da aka daura mata.
Ya kuma kara da cewa Iran tana daga cikin kasashen da suka sanya hannu a yarjeniyar NPT wacce ta bata samar amfanin da makamacin nukliya ta zaman lafiya. Banda haka irana tana son ta shiga tattaunawa da kasashen Turai don warware matsalar shirin makamashin nukliya ta kasar ba tare da an harba harsashi go guda ba.
Ana bangare babban sakataren MDD ya yaba da tunanin tattaunawa ba kai tsaye ba , sannan ya taya kasar bakin ciki kan gobarara da ta tashi a tashar jiragen ruwa ta Ali Ra’ei a bandar Abbas.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar Hamas Ta Bayyana Cewa Ba za ta Ajiye Makamanta ba Sai Bayan samar Da Kasar falasdinu
Kungiyar Hamas wacce takr iko da Gaza kuma take gwagwarmaya da HKI tun shekara ta 2023 a baya-bayan nan, ta bayyana cewa ba za ta ajiye makamanta ba sai an kafa kasar falasdinu mai zaman kanta, wanda yin watsi ne da bukatar HKI na shafe kungiyar daga doron kasa.
Shafin labarai na Internet Arab News na kasar Saudiya ya nakalto kungiyar tana fadar haka bayan da taron tattaunawa ta tsagaita budewa juna wuta na kwanaki 60 ya tashi baram-baram a birnin Doha na kasar Qatar.
Labarin ya kara da cewa, a ranar Talatan da ta gabata ce, kasashen Qatar da Masar suka amince da ra’ayin samar da kasashe biyu a kan kasar Falasdinu da aka mamaye, a matsayin hanya Tilo ta warware rikicin Falasdinawa da yahudawan HKI, sannan a lokacin ne Hamas zata mika makamanta ga gwamnatin jeka na yika ta Palasdinawa waccea take samun goyon bayan kasashen yamma da kasashen larabawa.
Amma kungiyar Hamas ta amsawa wadannan kasashe kan cewa kungiyar ba zata taba ajiye makamanta ba, sai bayan an kafa kasar Falasdinu mai cikekken yenci da kuma birnin Qudus a matsayin babban birnin Qasar.
HKI tana ganin duk wata yarjeniyar da za’a cimma da Hamas idan bai hada da karbe makamanta b aba abin amincewa ne gareta ba.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kungiyar Hamas Ta Wallafa Hotunan bidiyo Na Fursinan HKI tsare A Gaza August 3, 2025 Sojojin HKI, Daga Jiya Zuwa Yau lahadi Kadai Sun Kashe Falasdinawa 62 August 3, 2025 Pezeskkian Ya Ce: Suna Fatan Musayar Kasuwancin Tsakanin Iran Da Pakistan Ta Haura Dala Biliyan 10 August 2, 2025 Araqchi: Abokantaka Da Ke Tsakanin Iran Da Pakistan Wata babbar Jari Ce Nan Gaba August 2, 2025 Jaridar Isra’ila Ta Ce: Gwamnatin Mamayar Isra’ila Ta Sha Kashi A Yakin Gaza August 2, 2025 Dakarun Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Lod Da Ke Haramtacciyar Kasar Isra’ila August 2, 2025 Rahoton Majalisar Dinkin Duniya Ya Yi Gargadi Kan Barazanar Kungiyoyin ‘Yan Ta’adda A Afirka August 2, 2025 Shugaba Pezeshkiyan Ya Yi Juyayin Shahadar Haniya Bayan Shekara Guda Da Shahada August 2, 2025 MDD: HKI Ta Kashe Falasdinawa Fiye Da 100 A Cikin Kwanaki 2 A Lokacinda Suka Karban Abinci August 2, 2025 Mutanen Kasar Siriya Sun Fito Zanga-Zanga Yin Allawadai Da Kissan Alawiyya A Kasar August 2, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci