HausaTv:
2025-06-19@06:48:06 GMT

Iragchi Ya Zanta Ta Wayar Tarho Da Babban Sakataren MDD Antonio Guterres

Published: 4th, May 2025 GMT

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Argchi ya zanta ta wayar tarho da babban sakataren MDD Antonio Guterres inda ya fada masa inda aka kwana a tattaunawar da kasarsa take da Amurka ba kai tsaye ba.

Kamfanin dillancin labaran Ip na kasar Iran ya nakalto Arigchi yana fadawa babban sakatarin kan cewa akwai bukatar bangarorin biyu su yi gaske don cimma yarjeniya wacce kowa ya amince da ita.

  Wannan tattaunawar tana da muhimmanci a wajen Iran don itace zata fauuace makomar shirin nukliyar kasar Iran. Da kuma takunkuman zaluncin da Amurka ta dorawa kasar.

Tattaunawar dai tana nuna irin yadda Iran ta fifita tattaunawa da kuma hanayr diblomasiyya kan shiga wasu rigingimu wadanda basa da amfani.

Aragchi ya fadawa Goterres kan cewa Iran tana bukatar ta ci gaba shirinta na makamashin nukliya ta zaman lafiya. Sannan a dauke mata takunkuman zaluncin da aka  daura mata.

Ya kuma kara da  cewa Iran tana daga cikin kasashen da suka sanya hannu a yarjeniyar NPT wacce ta bata samar  amfanin da makamacin nukliya ta zaman lafiya. Banda haka irana tana son ta shiga tattaunawa da kasashen Turai don warware matsalar shirin makamashin nukliya ta kasar ba tare da an harba harsashi go guda ba.

Ana bangare babban sakataren MDD ya yaba da tunanin tattaunawa ba kai tsaye ba , sannan ya taya kasar bakin ciki kan gobarara da ta tashi a tashar jiragen ruwa ta Ali Ra’ei a bandar Abbas.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An garzaya da ’yan Isra’ila 154 asibiti bayan harin Iran

Isra’ila ta tabbatar cewa an garzaya da ’yan ƙasarta aƙalla 154 asibiti bayan sabbin hare-haren ramuwar gayya da Iran ta kawo mata.

Ma’aikatar lafiyar Isra’ila ta ce aƙalla mutum huɗu daga cikin waɗanda aka kai asibitin suna cikin halin rai-kwakwai-mutu-kwakwai, wasu biyar kuma na samun kulawa ta musamman saboda tsananin tashin hankali.

Alkaluman da ma’aikatar ta fitar sun nuna cewa mutum 130 daga cikin majinyatan sun samu raunuka marasa tsanani a sakamakon hare-haren.

Wannnan na zuwa ne a yayin da Iran ta ci gaba luguden rokoki a matsayin ramuwar gayya a sassan Isra’ila a a ranar Talata.

Isra’ila ta ce Iran ta lashe mata mutane akalla 24.

A ɗaya ɓangaren kuma Iran cewa harin tsokana da Isra’ila ta kai mata ya yi ajalin kimanin mutum 224.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kar a kuskura a shiga cikin yaƙin Iran da Isra’ila — MDD
  • Litar fetur za ta iya komawa N1,000 a Najeriya saboda yakin Isra’ila-Iran – Masana
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kwaso ‘Yan Nijeriya Da Suka Maƙale A Isra’ila Da Iran
  • Amurka na iya kashe jagoran addini na Iran don mun san inda yake — Trump
  • Iran ta kai hari hedikwatar hukumar leƙen asirin Isra’ila
  • An garzaya da ’yan Isra’ila 154 asibiti bayan harin Iran
  • Yaƙin Iran da Isra’ila: Amurka za ta tura jami’anta don tattaunawa da Tehran
  • Matatar man Isra’ila ta daina aiki bayan sabon harin Iran
  • Sin Ta Yi Kira Ga Iran Da Isra’ila Su Dauki Matakan Dakile Ruruwar Wutar Rikicinsu Nan Da Nan
  • Jami’an Tsaron Kan Iyakar Iran Sun Harbo Jiragen Masara Matuka 44 Na Sojojin H.K.Isra’ila