Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Esmaeil Baqaei, ya yi Allah wadai da kakkausar murya kan harin da jiragen yakin Isra’ila suka kai kan wani jirgin ruwa, da ke dauke da kayan abinci da na agaji zuwa zirin Gaza da ke gabar ruwan kasar Malta.

Esmaeil Baqaei ya yi tsakaci game da kisan kiyashin da ake yi a zirin Gaza, inda Ya ce, harin da aka kai kan jirgin ruwan mai dauke da kayan agaji, babban laifi ne, kuma ya zama ta’addanci.

Halin da ake ciki a Gaza ya kai intaha inda cikin sama da kwanaki 60, babu wani jirgin ruwa dauke da abinci, agajin jin kai, ko mai da ya isa zirin, lamarin da ya kara hadassa wahalhalu da tabarbarewar ayyukan jin kai a zirin wanda kuma ya shafi yara da iyalai da dama wadanda ke fuskantar yunwa.

Tun a ranar 7 ga Oktoba, 2023, Isra’ila ta fara kai farmaki Gaza, sannan lamarin ya tsanata bayan da Isra’ila ta yi fatali da yarjejeniyar tsagaita bude wuta da kungiyar Hamas.

Ya zuwa yanzu, sama da mutane 50,000 aka kashe a hare-haren da Isra’ila ta kai Zirin.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Isra ila ta

এছাড়াও পড়ুন:

UNICEF Tayi Gargadi Game Da Mawuyacin Hali Da Yara Ke Ciki A Gaza

Kakakin hukumar kula da kanana yaran ta majalisar dinkin duniya  tess ingram ta bayyana cewa yanayin da yara ke ciki a yankin gaza yayi muni sosai, inda sama da yara miliyan daya dake gaza suke bukatar taimakon gaggawa na ruwan sha da kuma abinci

Ingram ta fadi a wata hira da aka yi da ita cewa dubban yara a falasdinu suna kwana da yunwa kusan kowanne dare,  kuma akalla yara 650,000 ba su koma makaranta ba duk da yarjejeniyar dakatar da bude wuta da aka cimamma a baya –bayan nan tsakanin bangarori biyu,

Har ila yau ta bayyana batun dakatar da bude wuta a matsayin labari mai kyau, da ya kawo karshen ci gaba da lugudan wuta da israila ke yi kowanne lokaci da ya ci rayukan dubban yara kanana, sai dai ta jaddada cewa yarjejeniyar dakatar da bude wuta ba za ta wadatar ba dole ne sai an kawo karshen yunwa da kuma samar da ruwan sha ga sauran iyalai  yankin gaza.

A ranar 10 ga watan okotba ne yarjejeniyar dakatar da bude wuta ta fara aiki a gaza  amma duk da haka yanayin da ake ciki ya kara tsananta baka iya zuwa wasu yankuna da dama a yankin saboda ci gaba da kasancewar sojojin isra’ila a wajen.

Isra’ila tana ci gaba da keta yarjejeniyar da ta cimma da kungiyar Hamas, tana ci gaba da kai hare-hare da  harbe harbe kuma tana hana shigar da kayan agaji da ake bukata zuwa yankin na Gaza, kuma kashi 2 cikin 3 na adadin wadanda aka kashe mata ne da yara kanana.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Hamas Ta yi Watsi Da Zargin Da Amurka Tayi Mata Kan Batun Motocin Agaji A Gaza November 3, 2025 El-Zakzaki: Yakin Sudan Yana Kare Maslahar Kasashen Yamma ne Kawai November 3, 2025 Iran Ta Karbi Sako Kan Batun Komawa Teburin Tattaunawa Ba Kai Tsaye Ba November 3, 2025 Ministar Jin Dadin Jama’a ta Sudan: Mayakan RSF Sun Kashe Mata 300 Da Yi Wa 25 Fyade A El Fasher November 3, 2025 Pezeshkian: Bunkasa Masana’antar Makamashin Nukiliyar Iran Don Inganta Rayuwar Al’ummar Iran Ne November 2, 2025 Araqchi: Da Hadin Bakin Amurka, Gwamnatin Isra’ila ta kaddamar Da Hari Kan Kasar Iran November 2, 2025 Larijani: Iran Ba Ta Tsoron Gudanar Da Tattaunawa, Amma Ta Zama Mai Amfani November 2, 2025 Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza November 2, 2025 Kasar Qatar Ta Ba Da Tallafin Gaggawa Ga Al’ummar Sudan Bayan Gumurzun El-Fasher November 2, 2025 IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya November 2, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • UNICEF Tayi Gargadi Game Da Mawuyacin Hali Da Yara Ke Ciki A Gaza
  • Allah Ya yi wa Malam Nata’ala rasuwa
  • Araqchi: Da Hadin Bakin Amurka, Gwamnatin Isra’ila ta kaddamar Da Hari Kan Kasar Iran
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Maganin Nankarwa (3)
  • Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon
  • Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • HKI Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza Inda Take Kashe Falasdinawa
  • Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar