Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Esmaeil Baqaei, ya yi Allah wadai da kakkausar murya kan harin da jiragen yakin Isra’ila suka kai kan wani jirgin ruwa, da ke dauke da kayan abinci da na agaji zuwa zirin Gaza da ke gabar ruwan kasar Malta.

Esmaeil Baqaei ya yi tsakaci game da kisan kiyashin da ake yi a zirin Gaza, inda Ya ce, harin da aka kai kan jirgin ruwan mai dauke da kayan agaji, babban laifi ne, kuma ya zama ta’addanci.

Halin da ake ciki a Gaza ya kai intaha inda cikin sama da kwanaki 60, babu wani jirgin ruwa dauke da abinci, agajin jin kai, ko mai da ya isa zirin, lamarin da ya kara hadassa wahalhalu da tabarbarewar ayyukan jin kai a zirin wanda kuma ya shafi yara da iyalai da dama wadanda ke fuskantar yunwa.

Tun a ranar 7 ga Oktoba, 2023, Isra’ila ta fara kai farmaki Gaza, sannan lamarin ya tsanata bayan da Isra’ila ta yi fatali da yarjejeniyar tsagaita bude wuta da kungiyar Hamas.

Ya zuwa yanzu, sama da mutane 50,000 aka kashe a hare-haren da Isra’ila ta kai Zirin.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Isra ila ta

এছাড়াও পড়ুন:

Aikin Gina Tashar Jirgin Ƙasa A Kano Yana Ci Gaba Gadan-gadan

Faɗin ginin, wanda ya haura sukwaya mita 13,000, ya ƙunshi babban ginin tashar da ababen da ke tattare da shi, kuma zai kasance tashar da ta fi kowace girma a layin dogon da ake kira Kaka Reluwe.

 

Kaka Reluwe na nufin hanyar dogo daga KAduna zuwa KAno.

 

Kamfanin CCECC ya ce idan an gama aikin, zai taimaka gaya wajen haɓaka harkokin sufuri kuma ya kawo matuƙar sauƙi ga miliyoyin matafiya a ɓangaren Kano na hanyar jirgin.

 

Shi dai wannan layin dogo na Kaka Reluwe, hanya ce mai tsawon kilomita 204. Ta tashi daga Kaduna, ta bi ta Zariya, zuwa Kano.

 

Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ne ya ƙaddamar da ita a ranar 15 ga Yuli, 2021, sannan gwamnatin Bola Ahmed Tinubu tana ci gaba da aikin babu ƙaƙƙautawa don tabbatar da ta kammala ta a kan lokaci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wani harin makami mai linzami daga Yemen ya fada filin jirgin saman Ben Gurion na Isra’ila
  • Kungiyar Hizbullahi Ta Lebanon Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya Suka Kai Kan Kasar Siriya
  • Gaza : Kungiyar Euro-Med ta bukaci a binciki harin Isra’ila kan jirgin ruwan Freedom Flotilla
  • Falasdinawa 40 Ne suka Yi Shahada A Zirin Gaza Sakamakon Ta’addancin Sojojin Mamayar Isra’ila A Jiya Juma’a
  • HKI Ta Kai Hari Kan Jirgin Ruwan Tawagar Masu Rajin Kare Hakin Bil’adama Dauke Da Agaji Zuwa Gaza
  • Hamas Ta Yi Allah Wadai Da Matsayin Amurka Na Goyon Bayan Haramta Hukumar Kula Da ‘Yan Gudun Hijiran Falasdinawa Ta UN
  • Aikin Gina Tashar Jirgin Ƙasa A Kano Yana Ci Gaba Gadan-gadan
  • WHO, ta nuna kaduwa da abin da ke faruwa a Gaza
  • Iran ta yi Allah-wadai da sabon takunkumin da Amurka ta lafta mata