Iran ta yi Allah-wadai da harin da Isra’ila ta kai kan jirgin ruwan da ke jigilar abinci zuwa Gaza
Published: 4th, May 2025 GMT
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Esmaeil Baqaei, ya yi Allah wadai da kakkausar murya kan harin da jiragen yakin Isra’ila suka kai kan wani jirgin ruwa, da ke dauke da kayan abinci da na agaji zuwa zirin Gaza da ke gabar ruwan kasar Malta.
Esmaeil Baqaei ya yi tsakaci game da kisan kiyashin da ake yi a zirin Gaza, inda Ya ce, harin da aka kai kan jirgin ruwan mai dauke da kayan agaji, babban laifi ne, kuma ya zama ta’addanci.
Halin da ake ciki a Gaza ya kai intaha inda cikin sama da kwanaki 60, babu wani jirgin ruwa dauke da abinci, agajin jin kai, ko mai da ya isa zirin, lamarin da ya kara hadassa wahalhalu da tabarbarewar ayyukan jin kai a zirin wanda kuma ya shafi yara da iyalai da dama wadanda ke fuskantar yunwa.
Tun a ranar 7 ga Oktoba, 2023, Isra’ila ta fara kai farmaki Gaza, sannan lamarin ya tsanata bayan da Isra’ila ta yi fatali da yarjejeniyar tsagaita bude wuta da kungiyar Hamas.
Ya zuwa yanzu, sama da mutane 50,000 aka kashe a hare-haren da Isra’ila ta kai Zirin.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Isra ila ta
এছাড়াও পড়ুন:
Yaƙin Iran da Isra’ila: Amurka za ta tura jami’anta don tattaunawa da Tehran
Shugaban Ƙasar Amurka, Donald Trump ya ce yana neman ganin an kawo karshen rikicin nukiliyar ƙasar Iran gaba ɗaya, a yayin da aka shiga kwana na biyar a yaƙin da ya ɓarke tsakanin Iran da Isra’ila.Trump ya bayyana shirinsa na tura manyan jami’an ƙasarsa zuwa birnin Tehran domin tattaunawa da hukumomin Iran a game da lamarin.
Ya bayyana haka ne a yayin da yake hawa jirgi domin barin ƙasar Kanada, inda ya halarci taron ƙasashen G7.
A yayin taron, shugabannin ƙasahen sun bayyana Iran a matsayin barazana, da bai kamata a bari ta mallaki makaman nukiliya ba. A ɗaya bangaren kuma sun bayyana ’yancin Isra’ila na kare kanta.
Matatar man Isra’ila ta daina aiki bayan harin Iran Sarki ya yi barazanar hana yin Musulunci a garinsa bayan dodanni sun kai wa Musulmi hari NAJERIYA A YAU: Yadda Cin Ganyayyaki Ke Yi Wa ‘Yan Najeriya WahalaTrump wanda ya bar taron tun kafin a kammala ya bayyana cewa abin da ke gabansa na wuce batun tsagaita wuta da Amurka ke nema tsakanin Iran da Isra’ila.
Ya bayyana cewa ƙasashen biyu da a halin yanzu suke ci gaba da yi wa juna luguden bama-bamai ba su sassauta ba, amma ya sha nanata cewa akwai yiwuwar kawo ƙarshen rikicin da wuri, idan Iran ta amince da tayin da Amurka ta yi mata.
Makon jiya ne jiragen Isra’ila suka ƙaddamar da hare-haren ba-zata a Iran inda suka kashe wasu manyan kwamandoji da masana kimiyyar nukiliya.
Isra’ila ta yi iƙirarin karɓe ikon sararin samaniyar Iran, kuma za ta tsananta kai hare-hare a nan gaba.
Hare-haren sun halaka mutane da dama a sassan kasashen biyu.
Rahotanni a cikin dare sun nuna yadda na’urorin tsaron sararin samaniyar Iran ke kakkaɓo makamai a sassan ƙasar.
Rundunar juyin juya halin Musulunci na Iran ta bayyana cewa za ta sake harba tarin rokoki zuwa Isra’ila.