Iran ta yi Allah-wadai da harin da Isra’ila ta kai kan jirgin ruwan da ke jigilar abinci zuwa Gaza
Published: 4th, May 2025 GMT
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Esmaeil Baqaei, ya yi Allah wadai da kakkausar murya kan harin da jiragen yakin Isra’ila suka kai kan wani jirgin ruwa, da ke dauke da kayan abinci da na agaji zuwa zirin Gaza da ke gabar ruwan kasar Malta.
Esmaeil Baqaei ya yi tsakaci game da kisan kiyashin da ake yi a zirin Gaza, inda Ya ce, harin da aka kai kan jirgin ruwan mai dauke da kayan agaji, babban laifi ne, kuma ya zama ta’addanci.
Halin da ake ciki a Gaza ya kai intaha inda cikin sama da kwanaki 60, babu wani jirgin ruwa dauke da abinci, agajin jin kai, ko mai da ya isa zirin, lamarin da ya kara hadassa wahalhalu da tabarbarewar ayyukan jin kai a zirin wanda kuma ya shafi yara da iyalai da dama wadanda ke fuskantar yunwa.
Tun a ranar 7 ga Oktoba, 2023, Isra’ila ta fara kai farmaki Gaza, sannan lamarin ya tsanata bayan da Isra’ila ta yi fatali da yarjejeniyar tsagaita bude wuta da kungiyar Hamas.
Ya zuwa yanzu, sama da mutane 50,000 aka kashe a hare-haren da Isra’ila ta kai Zirin.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Isra ila ta
এছাড়াও পড়ুন:
Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansaninta a Kebbi
Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta a Ƙaramar Hukumar Yauri ta Jihar Kebbi a wani mataki don bunƙasa harkokin tsaron iyakokin ruwa.
Hakan na zuwa ne bayan da wata tawagar manyan jami’an sojojin ruwan suka kai ziyara gidan gwamnatin Jihar Kebbi.
Ɗaliban da aka sace a Binuwai sun kuɓuta ’Yan Najeriya miliyan 34 na cikin barazanar yunwaSojojin sun kai ziayarar ne ƙarƙashin jagorancin Rear Admiral Patrick Nwatu – wanda ya wakilci babban hafsan sojin ruwan ƙasar.
Rundunar ta ziyarci Kebbi ne domin duba yadda za ta samar da sansaninta a jihar.
Patrick Nwatu ya yi tir da harin ta’addanci a kogin Neja, yana mai cewa yankin ya zama maɓoyar masu safarar makamai da sauran masu aikata laifuka.
Rundunar sojin ruwan Najeriya ta ce ta kammala shirye-shiryen kafa sansanin sojin ruwa a garin Yauri da ke jihar.
Babban Hafsan sojin ruwa, Vice Admiral Emmanuel Ogalla ne ya bayyana hakan a wata ziyarar ban girma da suka kaiwa Gwamnan Kebbi, Nasir Idris a gidan gwamnati da ke Birnin Kebbi a ranar Alhamis.
Da yake jawabi yayin ziyarar, jagoran tawagar Rear Admiral Patrick Nwatu, ya ce ziyarar wani ɓangare ne na faɗaɗa dabarun teku na sojojin ruwan Najeriya.