Majalisar zartaswar jihar Kano ta amince da kashe Naira biliyan 51.5 wanda ba a taba ganin irinsa ba, domin muhimman ababen more rayuwa da ayyukan yi wa al’umma hidima a fadin jihar, a wani bangare na tsare-tsare na gwamnatin na bunkasa zamantakewa da tattalin arziki.

 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar bayan taron majalisar zartarwa karo na 27 da aka gudanar a gidan gwamnatin Kano.

 

A cewar sanarwar, majalisar ta ba da haske ga manyan ayyuka da yawa, da suka hada da manyan gyare-gyaren hanyoyi, shigar da tsarin zirga-zirga, fadada gine-ginen jama’a, da inganta wutar lantarki.

 

Wani abin lura a cikin amincewar akwai fitar da naira biliyan 5.4 domin gyaran tituna da kwalta da suka tashi daga gidan Mumbayya zuwa Mahadar Tal’udu, Gadon Kaya, titin Yahaya Gusau, da Titin Sharada.

 

An kuma ware Naira biliyan 3.4 don samar da fitilun masu amfani da hasken rana a fadin birnin Kano a karkashin shirin sabunta birane.

 

An amince da karin wasu kudade don gina titin Miller zuwa titin Mishan da kuma gyara wasu muhimman kayayyakin aikin gwamnati da suka hada da Sashen Albarkatun Ilimi na Kano da Gidan Gwamna da ke Kaduna.

 

Majalisar ta kuma amince da Naira Biliyan 1.46 don ingantawa da kuma zamanantar da ma’aikatar Wutar Lantarki da Sabunta Makamashi da ke cikin Sharada.

 

Sanarwar ta ce “Wadannan amincewar sun nuna kudurin gwamnatin na samar da ci gaba mai dorewa a birane da kuma inganta ayyukan jama’a.”

 

 

 

Abdullahi Jalaluddeen/Kano

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Ayukka

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Na Iran Ya Ce: Maganar ‘Yan Sahayoniyya Rudu Ne Maras Amfani

Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ya bayyana kalaman gwamnatin ‘yan sahayoniyya a matsayin wani rudu da ba shi da amfani da har zai yi tasiri a zaman tattaunawan Iran da Amurka Wanda ba na kai tsaye ba, yana mai cewa duk wani hari ko da karami ne za a kai kan Iran zai zama tamkar tartsatsin wuta da zai iya janyo tashin gobara da zai iya kona yankin gaba daya.

A jawabin da ya gabatar yayin taron kolin majalisar shawarar Musulunci ta Iran a yau Talata, Muhammad Baqir Qalibaf ya bayyana cewa: Firai ministan gwamnatin yahudawan sahayoniyya mai laifi ne mai zubar da jinin fararen hula, saboda neman hana mutuwarsa a fagen siyasa, kuma yanzu yana yin barazana ga al’ummar Iran mai girma. Qalibaf ya yi nuni da cewa, wannan mutum mai rauni yana son canza haryar tafiyarsa a kullum rana saboda tsoron kada a kama shi sakamakon kasancewarsa mai laifi da yafi zama abin ki a tarihin wannan zamani.

Qalibaf ya kara da cewa; Bayan shafe shekaru da dama Netanyahu yana yaudarar kafafen yada labarai, a halin yanzu gwamnatin yahudawan sahayoniyya ta fito fili kuma ta bayyana hakikanin fuskar wannan azzalumi ga duniya, musamman ga matasan Amurka da Turai. Qalibaf ya kara da cewa babu wani abin da wannan gwamnatin ta cimma sai kai hare-haren bama-bamai kan makarantu da asibitoci, kuma ba ta cimma burin da ta ayyana a farkon yakin ba, kuma halin da ake ciki yana da matukar rashin tabbas.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya Ta Raba Rigunan Kariya Ga Wasu Jihohin Najeriya.
  • Gwamnatin Jihar Za Ta Ci Gaba Da Bullowa Da Dubarun Bunkasar Ta
  • Al’umma Sun Shiga Fargaba Yayin Da Ake Zargin ‘Yan Bindiga Sun Kashe Limamin Da Suka Sace A Zamfara
  • Syria: Adadin Wadanda Aka Kashe A Rikicin Bangaranci Sun Kai 70
  • Kwastam Ta Kama Jirage Marasa Matuka Da Sauran Kayayyaki Da Darajarsu Ta Haura Naira Biliyan 921 A Legas
  • Ma’aikatar Sharia A Nan Iran Zata Bayyana Abinda ya farsu A Tashar Jiragen Ruwa Na Shahid Rajae
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Shirya Fara Tantance ‘Yan Fansho
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Na Iran Ya Ce: Maganar ‘Yan Sahayoniyya Rudu Ne Maras Amfani
  • Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026