Gwamnatin jihar Kwara ta sake jaddada kudirinta na kara bude kofa ga al’umma domin ci gaba da kuma sanya jihar ta yadda za ta yi tasiri a duniya ta hanyar sanya hannun jari mai inganci.

 

Kwamishinan Ayyuka na Jiha Injiniya. Abdulquawiy Olododo, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake gabatar da ayukkan ma’aikatar a taron manema labarai na wata 3 na farkon shekara ta 2025, wanda aka gudanar a dakin taro na ma’aikatar kudi, Ilorin.

 

A cewarsa jimillar ayyuka 46 da ake ci gaba da gudanarwa a cikin kwata na farko na shekarar 2025, daga cikin su 33 an kammala su baki daya, inda a yanzu haka ayyuka 11 ke ci gaba da gudana.

 

Ya kara da cewa, an bayar da sabbin ayyukan tituna guda 24 a shekarar 2025 kadai, inda 6 tuni aka kammala su.

 

Kwamishinan ya bayyana yadda ake ci gaba da gudanar da aikin titin Agbamu – Ila-Orangun, hanya ce mai matukar muhimmanci a tsakanin jahohin kasar da nufin bunkasa harkokin tattalin arziki da kuma inganta hanyoyin shiga tsakanin jihohin Kwara da Osun.

 

Kwamishinan ya kuma sanar da cewa, hukumar kashe gobara ta jihar, ta tanadi kadarorin da darajarsu ta kai ₦728,478,052,012, wanda hakan ke nuni da karfafa tsarin bayar da agajin gaggawa na gwamnati.

 

Ya ci gaba da cewa, aikin titin RAAMP mai tsawon kilomita 209.77 da ake yi ya samu lambar yabo ta kasa guda biyu – Best in Counterpart Funding and Best in General Disbursement – wanda ya nuna kwazon gwamnati.

 

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kwara

এছাড়াও পড়ুন:

Shugabannin Arewa Sun Tattauna Sabon Hanyar Ci Gaba – Minista Uba Maigari Ya Yaba

 

Ministan Ƙasa na Ci Gaban Yankuna, Uba Maigari Ahmadu, ya yaba wa ci gaba da tattaunawa tsakanin jami’an gwamnati da shugabannin arewa yana mai cewa wannan “tattaunawa ce mai tarihi kuma cike da ƙarfi,” yana nuna cewa hangen nesa na Shugaba Bola Tinubu ga Arewa ya fara samo asali kuma yana haifar da sakamako.

 

Yayin jawabi a taron gidauniyar tunawa da Sir Ahmadu Bello a rana ta biyu na zaman tattaunawa tsakanin gwamnati da alumma, ministan ya jaddada cewa wannan zama shi ne karo na farko a tarihin mulkin Najeriya inda ministoci, daraktocin hukumomi, shugabannin kwamitoci, da sauran manyan jami’an gwamnati daga Arewa suka “mika kansu don a yi musu tambayoyi” daga mutanen da suke yi wa hidima.

 

Ya ce gwamnati na da rubutattun nasarori da ake iya gani, yana bayyana wannan mataki a matsayin sabon hanya don samun amincewar jama’a, “wadanda su ne a ƙarshe suka fi rinjaye wajen zabe.”

 

Tattaunawar ta shafi fannoni da dama – tsaro na abinci, noma, ilimi, lafiya da ci gaban ababen more rayuwa – inda mahalarta suka amince cewa wadannan matsaloli suna da alaƙa sosai kuma suna bukatar kulawa cikin gaggawa.

 

Ministan ya bayyana wannan zama a matsayin “tattaunawar fannoni daban-daban don makomar Arewa,” yana mai cewa burin shi ne samar da tsare-tsare masu amfani ga birane da karkara.

 

Lokacin da aka tambaye shi yadda “hanyar gaba” za ta kasance, Ahmadu ya ce manufar gwamnati ba kawai yin magana ba ce, amma ta saurara, ta yi rubutu, kuma ta yi aiki.

 

Ya kara da cewa gwamnati na mai da hankali sosai kan batun sarƙoƙin samar da abinci, farfaɗo da noma da kare ‘yancin al’ummomin makiyaya.

 

A matsayin abin da ya kira “juyin hali,” Ahmadu ya tabbatar cewa gwamnati ta amince da karin kasafin kuɗi don shirye-shiryen ci gaban Arewa – abin da ya nuna gwamnati ba kawai alkawari take yi ba, har ma tana saka kuɗi a bayansa.

 

Sai dai ministan bai boye kalubalen da ke akwai ba, ciki har da matsin tattalin arziki, rikicin al’adu da harsuna, da ƙarin matsa lamba kan ƙasar noma saboda sauyin yanayi da yawaitar jama’a.

 

Ahmadu ya jaddada cewa wannan lokaci “sabuwar farawa” ce ga Arewa, wadda ke buƙatar haɗin kai tsakanin shugabanni, al’umma da hukumomin gwamnati.

 

Taron zai ci gaba na wasu kwanaki, inda za a gabatar da ƙarin rahotanni daga ma’aikatun gwamnati da hukumomi kamar North-East Development Commission don bayyana ci gaban ayyuka.

 

“Wannan abu ne game da gaskiya, amana, da sabuwar farawa ga Arewa,” in ji Ahmadu, yana tabbatar da cewa tattaunawar da ake yi yanzu za ta tsara makomar yankin.

 

COV: Khadija Kubau

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin
  • Gwamnatin Jigawa ta horas da malamai 20,000 fasahar sadarwar zamani
  • Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Shugabannin Arewa Sun Tattauna Sabon Hanyar Ci Gaba – Minista Uba Maigari Ya Yaba
  • Gwamnan Kaduna Ya Sauke Kwamishinan Yaɗa Labarai, Ya Maye Gurbinsa Da Maiyaki
  • Shugaban SUBEB Yayi Alkawarin Bayar Da Tallafin Ilimi A Jihar Nasarawa
  • Gwamnatin Jihar Kano Ta Kaddamar da Manufar Sauyin Yanayi
  • An shawarci Manoman Kwara Da Su Yi Taka-Tsan-Tsan Saboda Hasashen Ruwa Da Tsawa A Jihar
  • Gwamnatin Sakkwato Ta Sayo Manyan Tan-tan 250 Na Sama Da Naira Biliyan 22