Gwamnatin Jihar Za Ta Ci Gaba Da Bullowa Da Dubarun Bunkasar Ta
Published: 1st, May 2025 GMT
Gwamnatin jihar Kwara ta sake jaddada kudirinta na kara bude kofa ga al’umma domin ci gaba da kuma sanya jihar ta yadda za ta yi tasiri a duniya ta hanyar sanya hannun jari mai inganci.
Kwamishinan Ayyuka na Jiha Injiniya. Abdulquawiy Olododo, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake gabatar da ayukkan ma’aikatar a taron manema labarai na wata 3 na farkon shekara ta 2025, wanda aka gudanar a dakin taro na ma’aikatar kudi, Ilorin.
A cewarsa jimillar ayyuka 46 da ake ci gaba da gudanarwa a cikin kwata na farko na shekarar 2025, daga cikin su 33 an kammala su baki daya, inda a yanzu haka ayyuka 11 ke ci gaba da gudana.
Ya kara da cewa, an bayar da sabbin ayyukan tituna guda 24 a shekarar 2025 kadai, inda 6 tuni aka kammala su.
Kwamishinan ya bayyana yadda ake ci gaba da gudanar da aikin titin Agbamu – Ila-Orangun, hanya ce mai matukar muhimmanci a tsakanin jahohin kasar da nufin bunkasa harkokin tattalin arziki da kuma inganta hanyoyin shiga tsakanin jihohin Kwara da Osun.
Kwamishinan ya kuma sanar da cewa, hukumar kashe gobara ta jihar, ta tanadi kadarorin da darajarsu ta kai ₦728,478,052,012, wanda hakan ke nuni da karfafa tsarin bayar da agajin gaggawa na gwamnati.
Ya ci gaba da cewa, aikin titin RAAMP mai tsawon kilomita 209.77 da ake yi ya samu lambar yabo ta kasa guda biyu – Best in Counterpart Funding and Best in General Disbursement – wanda ya nuna kwazon gwamnati.
COV/ALI MUHAMMAD RABIU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kwara
এছাড়াও পড়ুন:
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato
Mataimakinsa kan harkokin majalisa Honarabul Attahiru Danmadi ne ya wakilci dan majalisar ya kuma tabbatarwa wadanda lamarin ya shafa kokarinsa kan daukar matakan da suka kamata domin tabbatar da tsaron rayukan su da dawowa da zaman lafiya a yankunan.
Garuruwan da ‘yan bindigar suka tarwatsa a gundumar Kuchi sun hada da Fakku, sha’alwashi, tulluwa da Rafin- gora a inda mutane bakwai suka rasa rai. A gundumar Jabo kuwa kauyukan da lamarin ya shafa su ne; Gesolodi, Hilya, Guraye, Guma, Chakai, Modo, Badariya, Tafki, Balera, Gudumawa da Rafin shinka.
“Mun girgiza kwarai da wannan halin da kuke ciki. A matsayina na wakilin ku, zan ci-gaba da kokarin da ya kamata a majalisa domin ganin jami’an tsaro sun kawo karshen wannan ta’addancin.”
Dan Majalisar ya ce ya gabatar da bukata ga Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Kasa domin tallafawa wadanda lamarin ya shafa kuma zai ci- gaba da bibiya domin ganin tallafin ya samu cikin lokaci.
Ya ce yana kokarin ganin rundunar sojoji ta kara tura wadatattun jami’ai tare da tallafa masu domin yakar ‘yan ta’addan da wanzar da zaman lafiya a yankunan.
Tallafin kayan abinci na gaggawa da dan majalisar ya bayar sun hada da buhuhuwan masara, gero, garin kwaki da kuma kuli- kuli.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp