Gwamnatin kasar Iran ta bayyana cewa samar da kasar Falasdinu mai cikekken yenci , kuma da dukkan birnin Qudus a matsayin babban birnin kasar, hakkin Falasdinawa ne wannan babu tattaunawa a kansa.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Jakadan kasar Iran na din din din a MDD Amir Said Iravani yana fadar haka, a jiya laraba, a lokacinda yake gabatar da jawabi a gaban kwamitin tsaro na majalisar.

Jakadan ya bukaci kungiyoyin Falasdinawa su hada kansu don duk wani sabani a tsakaninsu nasarace ga HKI.

Iranvani ya ce HKI tana ci gaba da aikata laifukan yaki a yankin Gaza da kuma yankin yamma da kogin Jordan, tare da tallafin Amurka da wasu kasashen yamma. Kuma tallafin da wadannan kasashen suka bawa HKI, kama daga makamai, kudade, tallafin siyasa da sauransu ne suka sa HKI ta ke samun karfin giuwan ci gaba da sabawa dokokin kasa da kasa.

Tun kusan watanni biyu da suka gabata ne HKI ta hana shigar kayakin abinci da wasu bukatun mutanen kasar Falasdun a gaza, wanda shi shi kaidai ya isa laifukan yaki da dama, wadanda suka sa dole na a hukunta HKI kan wadannan laifuffukan. Da kuma wadanda suka taimaka masu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran:  Makamin Nukiliya Ba Ya Cikin Akidar Tsaron Kasar Iran

Sakataren Majalisar koli ta tsaron kasar Iran wanda ya halarci taron kungiyar “Brics” a kasar Brazil ya bayyana cewa; Makaman Nukiliya ba su cikin akidar tsaron kasar Iran.

Ali Akbar Amhadiniyan ya kuma kara da cewa; Iran ba za ta amince da kin aiki da hakkokinta na cin moriyar fasahar makamashin Nukiliya a fagagen zaman lafiya ba.

Da yake Magana akan Falasdinu kuwa, sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran ya ce: “Amfani da karfi domin kai wa ga sulhu” da “Diflomasiyya ta dole” akidun siyasa ne masu hatsarin gaske, yana mai kara da cewa; ta hanyar shimfida adalci ne ake kai wa ga sulhu,haka nan kuma yin furuci da hakokin da suke halartattu.

Akan barazanar da wasu kasashe suke yi wa kungiyar ta “Brics kuwa Ahmadiyan ya ce; Hakan yana nuni ne da zurfin damuwa akan abinda Brics din za ta iya yi domin zama kungiya mai karfi a nan gaba a fagagen siyasa, tattalin arziki, da kuma al’adu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka Ta Kakabawa Kamfanonin Da Suka Hulda Da Iran Bangaren Man Fetur
  • Arif: A Shirye Muke Mu Sabunta Sana’o’in Sudan
  • Iran:  Makamin Nukiliya Ba Ya Cikin Akidar Tsaron Kasar Iran
  • Amurka ta sake laftawa wasu kamfaninin mai na Iran takunkumi
  • Iran Da Iraki Sun Ce An Kammala Shimfida Layin Dogo Daga Shalamcheh Zuwa Basra
  • Sabbin Bayanai Kan Fashe-Fashe Wasu Abubuwa A Tashar Jiragen Ruwan Kasar Iran
  • Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
  • Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
  • Shugaban Kasar Yana Maraba Da Masu Zuba Hannun Jari A Kasarsa Daga Kasashen Waje