Iran Tace Samar Da Kasar Falasdinu Mai Cikekken Yenci Ba Abin Tattaunawa Bane
Published: 1st, May 2025 GMT
Gwamnatin kasar Iran ta bayyana cewa samar da kasar Falasdinu mai cikekken yenci , kuma da dukkan birnin Qudus a matsayin babban birnin kasar, hakkin Falasdinawa ne wannan babu tattaunawa a kansa.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Jakadan kasar Iran na din din din a MDD Amir Said Iravani yana fadar haka, a jiya laraba, a lokacinda yake gabatar da jawabi a gaban kwamitin tsaro na majalisar.
Jakadan ya bukaci kungiyoyin Falasdinawa su hada kansu don duk wani sabani a tsakaninsu nasarace ga HKI.
Iranvani ya ce HKI tana ci gaba da aikata laifukan yaki a yankin Gaza da kuma yankin yamma da kogin Jordan, tare da tallafin Amurka da wasu kasashen yamma. Kuma tallafin da wadannan kasashen suka bawa HKI, kama daga makamai, kudade, tallafin siyasa da sauransu ne suka sa HKI ta ke samun karfin giuwan ci gaba da sabawa dokokin kasa da kasa.
Tun kusan watanni biyu da suka gabata ne HKI ta hana shigar kayakin abinci da wasu bukatun mutanen kasar Falasdun a gaza, wanda shi shi kaidai ya isa laifukan yaki da dama, wadanda suka sa dole na a hukunta HKI kan wadannan laifuffukan. Da kuma wadanda suka taimaka masu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Chadi: Majalisa ta amince a baiwa shugaban kasa damar ci gaba da Mulki har karshen rayuwa
Majalisar dokokin kasar Chadi ta amince da gyare-gyaren kundin tsarin mulkin kasar da zai tsawaita wa’adin shugabancin kasar daga shekaru biyar zuwa bakwai da kuma baiwa shugaban kasar damar ci gaba da mulki na tsawon wa’adi maras iyaka.
Majalisar dokokin kasar Chadi ta amince da sabon kundin tsarin mulkin kasar a ranar Litinin da kuri’u 171, yayin da aka kada kuri’a daya tilo da taki amincewa da hakan.
A ranar 13 ga watan Oktoba ne aka shirya kada kuri’ar karshe a majalisar dattawa, a cewar sanarwar da shugaban majalisar Ali Koloto Chaimi ya fitar, kamar yadda kamfanin dillancin labaran Reuters ya ruwaito. Sannan kuma shugaban kasar zai sanya hannu kan kundin tsarin mulkin sannan ya zama doka.
Shugaban kasar Chadi, Mahamat Idriss Deby ya karbi mulkin kasar ne bayan kisan mahaifinsa tsohon shugaba Idriss Deby, a lokacin da ya ziyarci sojojin da ke yaki da mayakan ‘yan tawaye a arewacin kasar a shekarar 2021.
Deby ya yi ikirarin samun nasara bayan zaben da aka gudanar bayan shekaru uku na mulkin soja a watan Mayun 2024, sannan kuma aka gudanar da zaben ‘yan majalisar dokoki a watan Disamba, wanda ya bai wa jam’iyya mai mulki rinjayen kujeru.
An samu cece-kuce game da sakamakon zaben, bayan da madugun ‘yan adawa kuma firaministan kasar Succe Massara ya yi ikirarin samun nasara, ikirarin da hukumar zaben kasar ta yi watsi da shi.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Bukaci Musulmi Su Goyi Bayan Yunkurin Kasa da Ka Na Kauracewa Isra’ila September 17, 2025 Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza September 17, 2025 Iran da Saudiyya sun bukaci hadin kan Musulmi game da halin da ake a yankin September 17, 2025 Duniya na tir da sabon farmakin Isra’ila kan Gaza September 17, 2025 Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza September 17, 2025 Akalla Falsdinawa 78 Ne Suka Yi Shahada A Yau A Gaza. September 16, 2025 Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaida Dake Yamen September 16, 2025 Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki 5 A Wajen Taron kere-kere . September 16, 2025 Iran Ta Bukaci IAEA Tayi Tir Da Harin Da Isra’ila Ta Kai A Tashoshin Nukiyarta. September 16, 2025 Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana September 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci