Ficewar Kawu a jam’iyyarmu zai kawo zaman lafiya – Shugaban NNPP na Kano
Published: 24th, April 2025 GMT
Jam’iyyar NNPP reshen Jihar Kano, ta mayar da martani da nuna jin daɗi ga ficewar Sanata Abdulrahman Kawu Sumaila, zuwa Jam’iyyar APC kwanan nan, inda ta ce ficewarsa za ta kawo zaman lafiya a jam’iyyar.
Daily Trust ta ruwaito cewa hakan na zuwa ne sa’o’i 24 bayan Sanata Kawu Sumaila ya bayyana ficewarsa daga Jam’iyyar NNPP zuwa APC.
Da yake zantawa da manema labarai a Kano, Shugaban NNPP na Jihar Kano, Hashim Sulaiman Dungurawa, ya yi watsi da muhimmancin tafiyar da jam’iyyar tare da Kawu, inda ya bayyana shi a matsayin, “Wani mai taurin kai” wanda kasancewarsa a jam’iyyar ya fi kawo cikas fiye da amfani.
“Ba mu yi mamaki ba saboda wani abu ne da muka daɗe muna tsammani, dangane da batun jam’iyyarmu, mun riga mun dakatar da shi saboda ba shi da wata ƙima da zai ƙara, shi ya sa ya ci gaba da zama ba amfanin a cikinta,” in ji Dungurawa.
Dungurawa ya bayyana cewa, ficewar Kawu Sumaila ba asara ce ga Jam’iyyar NNPP ba, sai dai wani mataki ne da ya dace da zai dawo da kwanciyar hankali a cikin jam’iyyar.
“A yanzu jam’iyyar za ta samu zaman lafiya, ya kasance mai taurin kai a cikin ’yan jam’iyyar, don haka ficewar shi yana nufin jam’iyyar za ta iya mayar da hankali kan abin da ya kamata ta yi, saɓanin lokacin da yake nan yana hargitsa jam’iyyar,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Sanata Abdulrahman Kawu Sumaila zaman lafiya a jam iyyar
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
A wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ta fitar, ta yi tir da harin na Isra’ila akan Iran tare da bayyana cewa, ya haifar da rikici a tsakanin bangarorin biyu da kuma musayar harba makamai masu linzami.
Gwamnatin ta Najeriya ta nuna bakin cikinta akan abinda ya faru, tare da kuma da yin kiran a tsagaita wutar yaki da gaggawa, da kai zuciya nesa.
Har ila yau, sanarwar ma’aikatar harkokin wajen ta Nigeria wacce kakakinta Kimiebi Imomotimi Ebienfa ya rattabawa hannu a yau Asabar,14 ga watan Yuni 2025, ta jaddada cewa; yaki ba zai maye gurbin tattaunawa ba, kuma hanyar diplomasiyya ce za ta kai ga samar da zaman lafiya mai dorewa, girmama juna da aiki da dokokin kasa da kasa.,