Rasha Ta Sanar Da Kashe Manyan Kwamandojin Sojin Ukraine Fiye Da 60 A Birnin Sumy Na Kasar Ta Ukraine
Published: 15th, April 2025 GMT
Ma’aikatar tsaron Rasha ta sanar da yin luguden wuta kan zaman taron shugabannin sojojin Ukraine a birnin Sumy da ke arewa maso gabashin Ukraine
Ma’aikatar tsaron kasar Rasha ta sanar da cewa, ta kai hari kan wani ofishin rundunar sojojin Ukraine da ke dauke da makamai masu linzami na Iskander a yayin wani zaman taron manyan sojojin kasar a birnin Sumy, inda aka kashe jami’ai sama da 60.
Ma’aikatar tsaron Rasha ta kara da cewa sojojin na Ukraine na ci gaba da amfani da fararen hula a matsayin garkuwa gare su, tare da kafa cibiyoyin soji da kuma shirya tarurruka tare da halartar sojoji a tsakiyar birni mai yawan jama’a, tare da yin nuni da cewa; Rasha ta kai harin ne kan wani taron kwamandojin sojojin Ukraine.
Ministan harkokin wajen Rasha Sergei Lavrov ya ce kasarsa na da shaidun da ke nuna cewa ana gudanar da taron shugabannin sojojin Ukraine da na yammacin Turai ne a wurin da aka kai hari a birnin Sumy.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: sojojin Ukraine
এছাড়াও পড়ুন:
Wani Fim Din Iran Mai Ya Sami Kyauta A Baje-Kolin Fina-finai Na Shanghai
Fim din Iran mai taken: Akharin Kuse Nahang” wanda Ramtin Balf ya shirya shi ya samu kyauta a baje kolin fina-finan ta Shangahi.
Shugaban ma’aikakar al’adu da koyarwar musulunci ta Iran a yankin Bu-Shehr Muhammad Hussain Zaduyan ya sanar da cewa; Fim din wanda na ilmantarwa ne, yana daga cikin fina-finai masu muhimmanci da aka fitar da shi a Iran.
Shi dai wannan bikin na baje kolin fina-finai a Shanghai an yi shi ne daga ranar 3 ga watan Yuli zuwa 7 ga gare shi a wannan shekarar ta 2025.
An yi wannan bikin ne na baje-koli ne a daidai lokacin da ake yin taron kungiyar “BRICS” da taron kasashen Asiya.
Zanduyani ya kuma ce; Fim din na Iran wanda yake Magana akan matsalar da ake fuskanta ta karewar wasu daga cikin halittun ruwa, kamar kifin “Shakes” ya sami kyautar a wurin wannan taron na baje koli wanda shi ne karo na 17.”
Karamin ofishin jakadancin Iran a kasar China wanda yake kula da yada ala’adun Iran, shi ne ya wakilci wanda ya shirya fim din wajen karbar kyautar da aka ba shi.