Shugaban Hukumar IAEA Ya Ce JMI Bata Da Makaman Nukliya
Published: 6th, April 2025 GMT
Rafael Grossi shugaban hukumar makamashin nukliya ta duniya (IAEA) ya bayyana cewa JMI bata da makamin Nukliya, sai dai tana dukkan kayan aikin da ake bukata, da kuma fasahar kera makamin idan tana bukatar yin hakan.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Grossi yana fadar haka a wata hira da yayi da tashar talabijin ta Agentina a yan kwanakin da suka gabata.
Abinda tambaya a nan itace tunda hukumar ta tabbatar da cewa a halin yanzu Iran bata da makaman Nukliya me yasa Amurka take tada hankali kuma take barazana ga kasar dangane da shirin ta na makamashin Nukliya al-hali bata da shi?
Grossi ya bayyana cewa al-amuran siyasa da kuma takurawa kasar da kasashen yamma suke yi shi ne yake ruruta rikicin da ke faruwa tsakanin Iran da kasashen yamma. Shugaban ya tabbatar da cewa gwamnatin JMI tana bada hadin kai ga masu binciken hukumar wadanda suke gudanar da bincike a dukkan cibiyoyin makamashin nukliya na kasar ta Iran.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta
A jiya Litinin ne dai gwamnatin kasar Holland ta sanar da hana wa minstocin tsaron kasa Itmir Bin Gafir, da na kudi, Bitsirael Smotrich shiga cikinta.
Kasar ta Holland ta zargi wadannan mutanen biyu da cewa suna ingiza sojojin HKI da yi wa Falasdinawa kisan kiyashi da kuma fadada yawan matsugunan ‘yan sahayoniya a yankunan da aka ce nan ne za a kafa Daular Falasdinawa.
Haka nan kuma gwamnatin kasar ta Holland ta kira yi jakadan HKI a birnin Hauge domin gargadinsa akan yanayin da ake ciki a Gaza, da cewa babu yadda za a iya ci gaba da jurewa akansa, ko kare dalilin jefa yankin cikin wannan halin.”
Wannan matakin na kasar Holland ya zo ne gabanin wani taro da tarayyar turai za ta yi a yau Talata domin jingine aikin tare da HKI a fagen nazari da bincike na ilimi, saboda ta ki tsagaita wutar yaki a Gaza.
Tun da fari, Fira ministan kasar Holland Dick Schoof ya wallafa a sharin X cewa; A yayin taron da kasashen turai za su yi, Kasarsa za ta yi matsin lamba akan ganin an dakatar da yarjejeniyar kasuwanci da HKI, haka nan kuma kakaba takunkumai akan shigar da kayanta na kasuwanci zuwa kasuwannin turai.
Fira ministan na kasar Holland ya ce, ya fada wa shugaban HKI Ishaq Herzog wannan matakin da suke son dauka ta hanyar tarayya turai.