JMI Ta Kaddamarda Sabbin Ci Gaban Da Ta Samu Da Fasahar Nukliya A Ranar Makamashin Nukliya Ta Kasar
Published: 6th, April 2025 GMT
Gwamnatin Kasar Iran ta bada sanarwan samun sabbin ci gaba a fagen fasaha da kuma kayakin da suka shafi makamashin Nukliya, wanda za’a baje kolinsa a ranar 9 ga watan Afrilu na wannan shekarar , wato ranar makamashin Nukliya ta kasa.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto mataimakin shugaban kasa kuma shugaban hukumar makamashin Nukliya ta kasar Iran Mohammad Eslami yana fadar haka a yau Lahadi.
Ranar makamashin Nukliya ta kasa a nan JMI dai, ita ce ranar da hukumar makamashin nukliya ta kasa take bayyana irin nasarori da kuma ci gaban da ta samu a fasahar nukliya da kuma kaddamar da abubuwan da ta samu tare da amfani da wannan fasahar a ko wace shekara. Ya zuwa yanzu dai JMI ta samar da abubuwa da sama wadanda ta yi amfani da sinadarin Uranium ko makamashin nukliya kimani 100 a cikin kasar. Wanda ya nuna irin ci gaban da ta samu, ta kuma samu a wannan fagen
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: makamashin nukliya ta kasa makamashin Nukliya ta kasa
এছাড়াও পড়ুন:
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
Babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin CMG, ya gabatar da labarin ganawar da aka yi jiya Alhamis tsakanin shugabannin Sin da Amurka a Busan na Korea ta Kudu, cikin harsuna 85. Kuma zuwa yau Juma’a, mutanen da suka karanta rahotanni masu alaka da ganawar ta hanyoyin watsa labarai na dandalin CMG sun kai miliyan 712. Haka kuma, kafafen watsa labarai na kasa da kasa 1678, sun wallafa tare da tura rahotanni da bidiyon labaran CMG na harsuna daban daban game da ganawar, har sau 4431.
Har ila yau a wannan rana, an gudanar taron tattaunawa na kasa da kasa kan bude kofa da kirkire kirkire da ci gaba na bai daya a kasar Uruguay, wanda CMG da hadin gwiwar ofishin jakadancin Sin dake kasar suka shirya a Montevideo babban birnin Uruguay. (Mai fassara: FMM)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA