Aminiya:
2025-05-30@08:44:31 GMT

Babu dokar da na karya saboda yin taro a mazaɓata — Natasha

Published: 1st, April 2025 GMT

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan da Majalisar Dattawan Nijeriya ta dakatar, ta ce taron barka da sallah da ta yi a mazaɓarta a yammacin Talata duk da haramta taruka da gwamnatin jihar ta yi ba karya doka ba ne.

Ana iya tuna cewa Gwamnatin Kogin dai ta hana duk wani nau’in taro ko gangami a jihar, saboda dalilin da ta ce na tsaro ne.

Haaland zai yi jinyar mako bakwai — Guardiola HOTUNA: Sarki Sanusi ya kai wa Abba ziyarar barka da Sallah

Kwamishinan ‘Yan sandan jihar, Miller Ɗantawaye, ya ce hana taron ya biyo bayan bayanan sirri da suka samu cewa za a samu barzanar tsaro, wanda ya tilasta gwamnatin jihar ɗaukar matakin.

Sai dai Natasha wadda ta isa jihar a wani jirgi mai saukar ungulu, ta bayyana wa magoya bayanta cewa tana da ’yancin kasancewa da mutanenta ta kuma yi shagalin farin ciki tare da su.

“A duk abin da za mu yi, mu sanya Allah a farko kuma mu shigar masa da buƙatunmu ta hanyar addu’a.

“Mijina ya kasance ɗaya daga cikin addu’o’ina da Allah Ya amsa. In banda haka ta yaya ni da ba kowa ba ce fa ce talaka daga ƙabilar Ebira na samu ƙarfin samun jirgin da zai kawo ni gida?

“Goyon bayan mijina ne ya kawo haka, kuma shi ke ciyar da ni gaba a koda yaushe.

“Tun jiya da na samu labarin za a rufe hanyoyi, aka kuma haramta taruka da jerin gwanon motoci a cikin gari na san cewa mu ne ake so a muzgunawa.

“Amma sai na faɗa wa kaina ai ba kakar siyasa ko yaƙin neman zaɓe ba ne yanzu.

“Don haka ni ba yaƙin neman zaɓe zan yi ba. Ni kaɗai ce zan shigo gari cikin mutane na, na yi shagalin bikin Sallah tare da su.

“Don haka babu wani laifi a ciki, babu dokar da na karya. A Najeriya muke. Ina da ’yancin shiga taruka da bukukuwa.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Iran, Da Kasashen Kungiyar BRICS Sun Gudanar Da Taro Kan Harkokin Tsaro A Mosco

An ngudanar da taron harkokin tsaro na kungiyar BRICS karo na 13TH inda wakilai da kasashen Iran da sauran kasashen kungiyar a birnin Mosco a ranar Laraba 28 ga watan Mayun da muke ciki.

Shafin yanar gizo na labarai AfricaNews ya bayyana cewa babbakan sakataren majalisar tsaro na kasar Iran Ali Akbar Ahmadian da Shugaban Bosnina serb Milorad Dodik da ministan tsaron kasar Korea ta Arewa Ri Chang-dae da kuma da wakilan tsaro daga kasashen duniya fiye da 100 ne suka sami halattan tarom na kwana guda.

A gefen taron a jiya Laraba sakataren majalisar tsaro na kasar Rasah Sergei Shoigu  ya gana da tokwaransa na kasar Iran Ahmadian inda suka tattauna kan al-amura da suka shafe harkokin tsaro tsakanin kasashen biyu.

An gudanar da taron ne daga 27-29 ga watan Mayu da muke ciki sannan wakilai 126 ne suka halarci taron.daga kasashen 104 wadanda suka kasance mambobi a kungiyoyin BRICS,Sco,ASEAN CIS da kuma kasashen kungiyar kasashen Larabawa , Au CSTO da wasu kungiyoyin  kasa da kasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince Da Dokokin Ilimin Noma da Gyaran Kotunan Gargajiya
  • NAHCON ta kammala jigilar maniyyata aikin hajjin 2025
  • Kasar Iran, Da Kasashen Kungiyar BRICS Sun Gudanar Da Taro Kan Harkokin Tsaro A Mosco
  • OPEC+ Ta Fara Shirin Ayyana Yawan Man Fetur Da Zata Haka Zuwa Sekara Ta 2027
  • Babu wanda ya tayar da bam a Abuja —Wike
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Kulla Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Kasar Indiya Don Habbaka Kiwon Dabbobi
  • Kamfanoni Mallakin Gwamnatin Sin Sun Samu Bunkasa Bisa Daidaito Cikin Watanni Hudu Na Farkon Bana
  • Kotu Ta Ci Tarar  El-Rufai Miliyan 900 Saboda Wani Laifi Da Ya Yi A 2019
  • Kasar Ireland Ta Yi Dokar Hana Shigar Da Kayan Da Aka Kera A ” Isra’ila” Cikinta
  • Sojojin Yahudawa sun Kashe Wani Matashi A Yankin Yamma Da Kogin  Jordan