Aminiya:
2025-09-17@21:59:02 GMT

Matsalar Tsaro: Shugaban Ƙaramar Hukuma ya tabbatar da haɗa kai da Sarakuna

Published: 13th, March 2025 GMT

Shugaban Karamar Hukumar Jama’a a Jihar Kaduna, Mista Peter Tanko Dogara, ya tabbatar da aniyarsa na yin aiki kafaɗa da kafaɗa da sarakunan gargajiya domin samar da tsaro da samar da ayyukan ci gaban ƙaramar hukumar.

Mista Dogara ya bayyana hakan ne yayin wata ziyarar aiki ta kwanaki biyu da ya kai zuwa ga masarautu shida da ke ƙaramar hukumar, inda ya jagoranci ɗaukacin jami’an majalisar ƙaramar hukumar don gudanar da ziyarar.

’Yan bindiga sun sace mutum 10 da raunata 2 a Kaduna Galibin ’yan Najeriya na neman muƙaman gwamnati don arzuta kansu — Obasanjo

A dai cikin makon nan ne Shugaban ƙaramar hukumar tare da tawagarsa suka ziyarci fadar Sarkin Kagoma, Mista Paul Zakkah Wyom; Sarkin Jama’a, Alhaji Muhammadu Isa Muhammadu; da Tum Nikyob, Mallam Tanko Tete. Ya bayyana godiyarsa tare da tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta aiwatar da aikinta cikin gaskiya da amana.

Ya jero wasu daga cikin nasarorin da majalisarsa ta cimma, ciki har da biyan kuɗin WAEC da JAMB ga ɗalibai 550 da kuma samar da guraben aiki ga wasu ‘yan yankin. Ya kuma jaddada ayyukan ci gaba da Gwamna Uba Sani ke aiwatarwa, tare da kira ga jama’a da su ci gaba da bayar da goyon baya da haɗin gwiwa.

A yayin da suke mayar da martani, sarakunan gargajiyan sun yaba wa shugaban ƙaramar hukumar bisa ziyarar da ya kawo, tare da gabatar masa da matsalolin da suka addabi yankunansu, ciki har da lalacewar hanyoyi, rashin ingantattun cibiyoyin kiwon lafiya, ƙarancin ruwan sha da kuma matsalolin tsaro.

Ziyarar ta ci gaba a ranar Laraba zuwa masarautun Zikpak, Godogodo, da kuma Barde, inda a  kowanne fada, Mista Dogara ya sake jaddada ƙudirinsa na kyautata rayuwar al’umma da kuma ƙarfafa zumunci tsakanin majalisar ƙaramar hukumar da sarakunan gargajiya.

Agwam Zikpak, Mista Josiah Kantyok, ya nanata buƙatar zaman lafiya a matsayin tushen ci gaba. Hakazalika, Sarkin Godogodo, Reɓerend Dakta Habila Sa’idu, ya roƙi majalisar da ta magance matsalolin kan iyaka tsakaninta da maƙwabtanta, yayin da Sarkin Barde, Mista Njebi Daniel Lemson, ya bayyana damuwarsa kan matsalar tsaro da ke addabar yankinsa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Karamar Hukumar Jama a ƙaramar hukumar

এছাড়াও পড়ুন:

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Hukumar NDLEA ta bayyana cewa wata ƙungiyar masu safarar miyagun ƙwayoyi ce a filin jirgin sama na Kano ta boye jakunkunan ƙwayoyi a cikin kayan matafiyan.

An kama shugaban ƙungiyar, Ali Abubakar Mohammed (wanda aka fi sani da Bello Karama), tare da wasu abokan aikinsa.

Hukumar ta ce mutanen ukun ba su da laifi kuma an zalunce su ne kawai.

An saki su ne bayan bincike da kuma ƙoƙarin diflomasiyya na tsawon makonni.

Lamarin ya tayar da hankali kan tsaro a filayen jirgin sama a Nijeriya da yadda masu aikata laifuka ke amfani da fasinjoji marasa laifi.

Hukumar ta ce za a ɗauki ƙarin matakai don hana faruwar irin wannan lamari.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 
  • Larijani: Iran Da Saudiyya Za Su Bunkasa Aiki Tare A Fagagen Kasuwanci Da Tsaro
  • Hukumar Tarayyar Turai Ta Gabatar Da Shawarar Jingine Aiki Da Yarjejeniyar KAsuwanci Da HKI
  • Karamar Hukumar Birnin Kano Ta Kaddamar Da Kula Da Lafiyar Ido Kyauta
  • Chadi:  Majalisa ta amince a baiwa shugaban kasa  damar ci gaba da Mulki har karshen rayuwa
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta