Matsalar Tsaro: Shugaban Ƙaramar Hukuma ya tabbatar da haɗa kai da Sarakuna
Published: 13th, March 2025 GMT
Shugaban Karamar Hukumar Jama’a a Jihar Kaduna, Mista Peter Tanko Dogara, ya tabbatar da aniyarsa na yin aiki kafaɗa da kafaɗa da sarakunan gargajiya domin samar da tsaro da samar da ayyukan ci gaban ƙaramar hukumar.
Mista Dogara ya bayyana hakan ne yayin wata ziyarar aiki ta kwanaki biyu da ya kai zuwa ga masarautu shida da ke ƙaramar hukumar, inda ya jagoranci ɗaukacin jami’an majalisar ƙaramar hukumar don gudanar da ziyarar.
A dai cikin makon nan ne Shugaban ƙaramar hukumar tare da tawagarsa suka ziyarci fadar Sarkin Kagoma, Mista Paul Zakkah Wyom; Sarkin Jama’a, Alhaji Muhammadu Isa Muhammadu; da Tum Nikyob, Mallam Tanko Tete. Ya bayyana godiyarsa tare da tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta aiwatar da aikinta cikin gaskiya da amana.
Ya jero wasu daga cikin nasarorin da majalisarsa ta cimma, ciki har da biyan kuɗin WAEC da JAMB ga ɗalibai 550 da kuma samar da guraben aiki ga wasu ‘yan yankin. Ya kuma jaddada ayyukan ci gaba da Gwamna Uba Sani ke aiwatarwa, tare da kira ga jama’a da su ci gaba da bayar da goyon baya da haɗin gwiwa.
A yayin da suke mayar da martani, sarakunan gargajiyan sun yaba wa shugaban ƙaramar hukumar bisa ziyarar da ya kawo, tare da gabatar masa da matsalolin da suka addabi yankunansu, ciki har da lalacewar hanyoyi, rashin ingantattun cibiyoyin kiwon lafiya, ƙarancin ruwan sha da kuma matsalolin tsaro.
Ziyarar ta ci gaba a ranar Laraba zuwa masarautun Zikpak, Godogodo, da kuma Barde, inda a kowanne fada, Mista Dogara ya sake jaddada ƙudirinsa na kyautata rayuwar al’umma da kuma ƙarfafa zumunci tsakanin majalisar ƙaramar hukumar da sarakunan gargajiya.
Agwam Zikpak, Mista Josiah Kantyok, ya nanata buƙatar zaman lafiya a matsayin tushen ci gaba. Hakazalika, Sarkin Godogodo, Reɓerend Dakta Habila Sa’idu, ya roƙi majalisar da ta magance matsalolin kan iyaka tsakaninta da maƙwabtanta, yayin da Sarkin Barde, Mista Njebi Daniel Lemson, ya bayyana damuwarsa kan matsalar tsaro da ke addabar yankinsa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Karamar Hukumar Jama a ƙaramar hukumar
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
Daga Usman Muhammad Zaria
Majalisar Zartarwa ta Jihar Jigawa ta amince da bayar da rancen kudi ga hukumar gidaje ta jihar domin gina gidaje 52 a Dutse.
A cikin wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed ya fitar, ya bayyana cewa gidajen za su kunshi masu dakuna uku da kuma dakuna biyu kowanne.
Ya ce aikin zai kasance a gaban tsohuwar unguwar majalisar dokoki, kusa da hanyar wucewa ta Jami’ar Tarayya da je Dutse, a matsayin wani shiri na asusun gina gidaje karkashin ma’aikatar gidaje, ci gaban birane da tsare-tsaren yankuna, ta hannun hukumar gidaje ta jihar.
Alhaji Sagir ya bayyana cewa, wannan mataki na nuna kudirin gwamnati wajen magance matsalar gidaje a babban birnin jihar, kara habaka ci gaban birane, tare da samar da ayyukan yi ga matasan jihar.
Ya ce an tsara wannan asusu ne domin tabbatar da dorewa, ta yadda za a ci gaba da zuba jari a ayyukan samar da gidaje masu araha a fadin jihar.
Haka kuma ya kara da cewa, gwamnatin jihar tana da kudirin ci gaba da inganta rayuwar al’ummarta, ta hanyar ayyuka masu amfani da jama’a, da ke inganta walwala, karfafa tattalin arziki, da tallafa wa matasa.
Kwamishinan ya kuma bayyana cewa, majalisar ta amince da bayar da kwangilar gyara da inganta gidan baki guda biyu (Malam Adamu Chiroma House da kuma Senator Francis Ella House) da ke cikin G9 Quarters a Dutse, da kudin sama da naira miliyan 219.7.
Ya ce aikin zai haɗa da cikakken gyara da inganta gine-ginen, gyaran hanyoyin ruwa da kuma girka tankokin ruwa ga kowanne daga cikin gidajen biyu.
Ya ce hakan na da nufin tabbatar da wadataccen ruwan sha mai dorewa a wuraren.
Alhaji Sagir Musa Ahmed ya kara da cewa, amincewar da aka yi da wannan kwangila na nuna jajircewar gwamnatin jihar wajen kula da dukiyar jama’a da kuma tabbatar da cewa gine-ginen gwamnati suna cikin yanayi mai kyau da nagarta.