A bara, alkaluman tattalin arziki na GDP na kasar Sin sun kai yuan triliyan 134.9, inda aka samu karuwar kaso 5 cikin dari, lamarin da ya sa shi kasancewa tattalin arziki mafi saurin ci gaba cikin kasashen duniya masu karfin tattalin arziki. Ci gaban da ake samu na ingantuwar tattalin arzikin kasar ya haifar da tarin alfanu ga jama’a.

Wani nazari da ya samu amsa daga mutane 25,883 daga kasashe 41 da kafar yada labarai ta CGTN ta gudanar, ya nuna cewa, sama da kaso 80 na wadanda suka bayar da amsa, sun yaba da tsarin ci gaban kasar Sin dake mayar da hankali kan moriyar al’umma, tare kuma da amincewa da ingancin salon shugabancin gwamnatin kasar Sin.

A shekarar 2024, mizanin aikin yi da na farashin kayayyaki sun kasance kan wani mataki mai daidaito, inda aka samar da guraben ayyukan yi miliyan 12.56 a birane, kana kudin shigar kowanne dan kasa ya karu da kaso 5.1. Baya ga haka, an karfafa tsare-tsaren bayar da ilimin tilas da kula da tsoffi da kiwon lafiya da sauran harkokin al’umma.

Ban Ji Dadin Zaman PSG Ba, Messi Manchester United Na Son Lashe Firimiya A Shekarar 2028

Cikin nazarin da CGTN ta gudanar, masu bayar da amsa sun yaba matuka da ingancin shugabancin gwamnatin kasar Sin, inda kaso 78.8 suka ce an cimma gagarumar nasara a harkar bayar da ilimi, kaso 70.1 sun yaba da yadda aka samu karuwar kudin shigar jama’a, kaso 63.4 kuma, sun yaba ne da ingantuwar muhallin rayuwa. Haka kuma, kaso 61 sun yaba da ingantuwar tsarin kiwon lafiya yayin da kaso 58.1 suka yaba da ingantuwar yanayin muhallin halittu. Wasu kaso 62.7 kuma sun ce fa’idojin da manufofin Sin ke da su na da muhimmanci wajen bayar da tabbaci ga ingantaccen tsarin shugabanci a kasar.

An samu wadannan alkaluma ne daga nazarce-nazarce biyu da kafar CGTN da jami’ar Renmin ta kasar Sin suka gudanar ta hannun cibiyar bincike kan harkokin kasa da kasa a sabon zamani, inda suka mayar da hankali kan “Yanayin Zama a Kasar Sin” da “Zamanatar da Kasar Sin”. Masu bayar da amsar sun hada da mutanen yankin arewacin Amurka da nahiyar Turai da Afrika da Oceania da kudu maso gabashin Asiya da gabashi da kudu da tsakiyar Asiya da kuma yankin Gabas ta Tsakiya. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: sun yaba da

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kungiyar ECOWAS  Ya Gana Da Shugaban Mulki Soji Na Kasar Guinea Bissau

Shugaban kungiyar kula da tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika kuma shugaban kasar saliyo Julius mada Bio yace ya tattauna da shugaban mulkin soji da ya yi juyin mulki a kasar Guinea Bissau , a kokarin da suke yi na ganin an yi aiki da kundin tsarin mulki a yankin na yammacin Afrika.

A cikin jawabin da ya wallafa a shafinsa na X bio ya fadi cewa ganawar ta su ta zo ne bayan kudurin da kungiyar ta ECOWAS ta fitar a taron da ta gudanar kan irin mataken da zaa dauka game da batun juyin mulki da aka yi a kasar Guinea Bissau a makon jiya.

Shiga tsakani a rikicin kasar Guinea Bissau ya zo ne sakamakon rashin zaman lafiya na siyasa da kuma tarihin juyin mulkin soja a kasar, tun bayan samun yanci kai a shekara ta 1974 , guinea Bissau ta sha fama da yankewar harkokin mulkin demukuradiya akai –akai.

Tshon shugaban Nigeria Goodlock Jonathan wanda ya jagoranci tawagar ECOWAS don sa ido kan yadda zaben ke gudana ya sanya alamar tambaya game da hakikanin juyin mulki da sojoji suka yi , yace wani shiri ne tsakanin shugaban kasar Embalo domin kaucewa rashin nasara a zaben da aka yi.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka An Bude Taron Bikin Cika Shakaru 41 Da Kafa Kungiyar Tattalin Arziki Ta ECO A nan Tehran December 2, 2025 Araghchi: Halayyar Amurka ce yin matsin lamba maimakon diflomasiyya a dangantaka ta kasa da kasa December 2, 2025 Aljeriya: Taron Kasashen Afirka Don Amincewa Da Mulkin Mallaka A Matsayin Laifi December 2, 2025 Lebanon: An Gudanar Da Taron Musulunci da Kiristanci a Beirut tare da halartar Paparoma December 2, 2025 Chuck Schumer: Trump Ba Shi da Ikon Kaddamar da Yaki Kan Venezuela December 2, 2025 Najeriya: Matatar Dangote Za Ta Mika Tataccen Mai Lita Biliyan 1.5 A Watan Disamba December 2, 2025 Ramaphosa ya yi watsi da barazanar Trump na ware Afirka ta Kudu daga G20 December 2, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 165 December 1, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan 164 December 1, 2025 Baqaei: Amurka Ce Babbar Barazana Ga Zaman Lafiya Da Tsaro A Duniya December 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƙudirin dokar hukuncin kisa ga masu satar mutane ya tsallake karatu na biyu
  • An Ga Sojojin Ruwa Na Amurka A Kasar Puerto Rico A Shirinta Na Mamayar Venezuela
  • Har yanzu ban bar yin waqa ba-Yusuf Lazio
  • Nigeria Ta Bai Wa Dan Takarar Shugabancin Kasar Guine Bissau Mafakar Siyasa
  • Shugaban Kungiyar ECOWAS  Ya Gana Da Shugaban Mulki Soji Na Kasar Guinea Bissau
  • ’Yan ta’adda sun kashe ɗan sanda a gidan DPO a Jigawa
  • Baqaei: Amurka Ce Babbar Barazana Ga Zaman Lafiya Da Tsaro A Duniya
  • Paparoma Leo Na 14 Yana Ziyarar Aiki Na Kwanaki 3  A Kasar Lebanon
  • Wani Dan Adawa Da Gwamnatin Paul Biya Ya Mutu A Gidan Yari A Kasar Kamaru
  • Sarkin Musulmi ya buƙaci gwamnonin Arewa suke saurarar ƙorafin jama’a