A bara, alkaluman tattalin arziki na GDP na kasar Sin sun kai yuan triliyan 134.9, inda aka samu karuwar kaso 5 cikin dari, lamarin da ya sa shi kasancewa tattalin arziki mafi saurin ci gaba cikin kasashen duniya masu karfin tattalin arziki. Ci gaban da ake samu na ingantuwar tattalin arzikin kasar ya haifar da tarin alfanu ga jama’a.

Wani nazari da ya samu amsa daga mutane 25,883 daga kasashe 41 da kafar yada labarai ta CGTN ta gudanar, ya nuna cewa, sama da kaso 80 na wadanda suka bayar da amsa, sun yaba da tsarin ci gaban kasar Sin dake mayar da hankali kan moriyar al’umma, tare kuma da amincewa da ingancin salon shugabancin gwamnatin kasar Sin.

A shekarar 2024, mizanin aikin yi da na farashin kayayyaki sun kasance kan wani mataki mai daidaito, inda aka samar da guraben ayyukan yi miliyan 12.56 a birane, kana kudin shigar kowanne dan kasa ya karu da kaso 5.1. Baya ga haka, an karfafa tsare-tsaren bayar da ilimin tilas da kula da tsoffi da kiwon lafiya da sauran harkokin al’umma.

Ban Ji Dadin Zaman PSG Ba, Messi Manchester United Na Son Lashe Firimiya A Shekarar 2028

Cikin nazarin da CGTN ta gudanar, masu bayar da amsa sun yaba matuka da ingancin shugabancin gwamnatin kasar Sin, inda kaso 78.8 suka ce an cimma gagarumar nasara a harkar bayar da ilimi, kaso 70.1 sun yaba da yadda aka samu karuwar kudin shigar jama’a, kaso 63.4 kuma, sun yaba ne da ingantuwar muhallin rayuwa. Haka kuma, kaso 61 sun yaba da ingantuwar tsarin kiwon lafiya yayin da kaso 58.1 suka yaba da ingantuwar yanayin muhallin halittu. Wasu kaso 62.7 kuma sun ce fa’idojin da manufofin Sin ke da su na da muhimmanci wajen bayar da tabbaci ga ingantaccen tsarin shugabanci a kasar.

An samu wadannan alkaluma ne daga nazarce-nazarce biyu da kafar CGTN da jami’ar Renmin ta kasar Sin suka gudanar ta hannun cibiyar bincike kan harkokin kasa da kasa a sabon zamani, inda suka mayar da hankali kan “Yanayin Zama a Kasar Sin” da “Zamanatar da Kasar Sin”. Masu bayar da amsar sun hada da mutanen yankin arewacin Amurka da nahiyar Turai da Afrika da Oceania da kudu maso gabashin Asiya da gabashi da kudu da tsakiyar Asiya da kuma yankin Gabas ta Tsakiya. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: sun yaba da

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana November 17, 2025 Daga Birnin Sin An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing November 17, 2025 Daga Birnin Sin Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO November 17, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Kwara ta rufe makarantu a kananan hukumomi 4 saboda matsalar tsaro
  • Sudan ta yaba da kokarin Amurka da Saudiyya na kawo karshen rikicin kasar
  • Daraktar Hukumar IAEA Ya Ce: Suna Tuntubar Juna Da Iran Kuma Masu Bincikensu Sun Kamo Kasar
  • Kotu A Gabon Ta Yanke Hukuncin Dauri A Kurkuku Kan Jami’an Tsohuwar Gwamnatin Kasar
  • Tankin ruwa ya kashe mutum 4, wasu sun jikkata a Jigawa
  • Kasar Maziko Tayi Watsi Da Shirin Trump Na Kai Harin Soji Kan Iyakar Kasar.
  • Kimanin Falasdinawa 2 Ne Suka yi Shahada Sakamakon Harin Isra’ila  A  Ainul Hilwa
  • Nijar: An Dakatar Da Ayyukan Kungiyoyin Agaji Da Dama
  • Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 
  • Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana