An kama korarren jami’in tsaro da ke sayar wa ’yan ta’adda makamai
Published: 6th, March 2025 GMT
’Yan sanda sun kama wani korarren jami’in shige da fice a yayin da yake kokarin sayar da makamai Ga ’yan ta’adda.
Kwamishinan ’Yan Sanda na Babban Birnin Tarayya, Olatunji Rilwan Disu, ya bayyana cewa an kama jami’in ne a hanyarsa ta kai wa ’yan ta’addan bindigogi a yankin Zuma da ke Ƙaramar Hukumar Bwari.
Da yake jawabi a hedikwatar rundunar, CP Olatunji Rilwan, ya bayyana cewa dubun korarren jami’in tsaron ta cika ne a ranar 27 ga watan Fabrairu, 2025.
Ya bayyana cewa jami’an rundunar yaki da masu garkuwa da mutane ƙarƙashin jagorancin OC Mustapha Muhammad ne suka kama shi, bayan samun bayanan sirri.
NAJERIYA A YAU: Me Ya Sa ’Yan Najeriya Ba Su Ga Ragi A Farashin Man Fetur Ba? Abubuwa 11 da ba a sakaci da su a Ramadan — Sheikh DaurawaDisu wanda ke bayani kan ayyukan rundunar daga watan Janairu zuwa Maris na 2025, ya ce an ƙwato wasu sabbin manyan bindigogi biyu ƙirar CZ Scorpion EVO 3 A1 a hannun wanda ake zargin.
Ya bayyana cewa rundunar tana tsare da wanda ake zargin yana amsa tambayoyi
Ya kara da cewa rundunar yaƙi da masu garkuwa da mutanen ta kuma halaka wasu ’yan bindiga bakwai a wani samamen da ta kai maɓoyar ɓata-garin a ƙauyen Gidan-Dogo da Daji Kweri da ke kan iyakar Abuja da Jihar Neja.
Ya ce an kama ’yan bindiga ɗauke da bindigogi ƙirar AK47da sauran wasu makamai a yankunan.
AA cewarsa, jimillar ’yan fashi da makami 59 da masu garkuwa da mutane tara da masu kai musu bayanai 10 ne dubu su ta cika a tsawon lokacin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Tsaro Ya bayyana cewa
এছাড়াও পড়ুন:
Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5
Bayanin da ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS ya yi a baya-bayan nan game da hasashe kan tattalin arzikin kasar Sin cikin shekaru biyar masu zuwa ya jawo hankalin duniya sosai. Kuma sakamkon binciken jin ra’ayoyin jama’a da CGTN na babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin wato CMG ya yi a tsakanin masu bayyana ra’ayoyi 47,000 a kasashe 46 daga shekarar 2023 zuwa 2025, ya nuna jama’ar sun nuna yakini game da karfi da juriyar tattalin arzikin kasar Sin.
Binciken ya nuna cewa, yawancin masu bayyana ra’ayoyin daga sassan duniya suna da kyakkyawan fata ga tattalin arzikin kasar Sin wajen samun bunkasa mai kyau a dogon lokaci, inda amincewarsu ta kai kashi 74.7 bisa dari, da 81.3 bisa dari, da kuma 81.9 bisa dari cikin shekaru uku a jere.
Binciken da aka yi a bana ya kuma nuna cewa, masu bayyana ra’ayoyin suna da kwarin gwiwa game da samun damammaki masu kyau a kasuwar Sin a cikin yanayin kasa da kasa mai sarkakiya da tashe-tashen hankula. A cikinsu akwai kashi 79.8 bisa dari da suka bayyana cewa, babbar kasuwar Sin ta ba da muhimman damammaki ga kasashen da suke gudanar da kasuwanci a ciki.(Safiyah Ma)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp