Aminiya:
2025-05-01@00:49:36 GMT

An kama korarren jami’in tsaro da ke sayar wa ’yan ta’adda makamai

Published: 6th, March 2025 GMT

’Yan sanda sun kama wani korarren jami’in shige da fice a yayin da yake kokarin sayar da makamai Ga ’yan ta’adda.

Kwamishinan ’Yan Sanda na Babban Birnin Tarayya, Olatunji Rilwan Disu, ya bayyana cewa an kama jami’in ne a hanyarsa ta kai wa ’yan ta’addan bindigogi a yankin Zuma da ke Ƙaramar Hukumar Bwari.

Da yake jawabi a hedikwatar rundunar, CP Olatunji Rilwan, ya bayyana cewa dubun korarren jami’in tsaron ta cika ne a ranar 27 ga watan Fabrairu, 2025.

Ya bayyana cewa jami’an rundunar yaki da masu garkuwa da mutane ƙarƙashin jagorancin OC Mustapha Muhammad ne suka kama shi, bayan samun bayanan sirri.

NAJERIYA A YAU: Me Ya Sa ’Yan Najeriya Ba Su Ga Ragi A Farashin Man Fetur Ba? Abubuwa 11 da ba a sakaci da su a Ramadan — Sheikh Daurawa

Disu wanda ke bayani kan ayyukan rundunar daga watan Janairu zuwa Maris na 2025, ya ce an ƙwato wasu sabbin manyan bindigogi biyu ƙirar CZ Scorpion EVO 3 A1 a hannun wanda ake zargin.

Ya bayyana cewa rundunar tana tsare da wanda ake zargin yana amsa tambayoyi

 

Ya kara da cewa rundunar yaƙi da masu garkuwa da mutanen ta kuma halaka wasu ’yan bindiga bakwai a wani samamen da ta kai maɓoyar ɓata-garin a ƙauyen Gidan-Dogo da Daji Kweri da ke kan iyakar Abuja da Jihar Neja.

Ya ce an kama ’yan bindiga ɗauke da bindigogi ƙirar AK47da sauran wasu makamai a yankunan.

AA cewarsa, jimillar ’yan fashi da makami 59 da masu garkuwa da mutane tara da masu kai musu bayanai 10 ne dubu su ta cika a tsawon lokacin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Tsaro Ya bayyana cewa

এছাড়াও পড়ুন:

 Manyan Malaman Roman Katolika Sun Fara Taron Zabar Paparoma

Manyan malaman addinin darikar Roman Katolika za su fara Shirin zabar shugaban darikar tasu a fadar Vatican

Adadin manyan malaman addinin masu mukamin “Cardinal” 130 ne za su taru a fadar Vatican, domin su zabi wanda zai maye gurbin Paparoma Farancis da ya rasu.

Sai dai masu kusancin da fadar ta Vatican suna bayyana cewa, da akwai batutuwa da dama da su ka raba kawunan manyan malaman addinin na Roman Katolika da  su ka batun auren jinsi, da rawar da mata za su taka a karkashin inuwar cocin.

Sai dai kuma wani mai sharhi akan abubuwan da su ka shafi cocin, Reese ya bayyana cewa, masu zaben za su mayar da hankali ne akan wanda zai kare ayyukan da mamacin Paparoma Francis ya bari.

Tare da cewa babu kafa ta yin yakin neman zabe a tsakanin masu mukamin na Cardinal, sai dai da akwai wasu siffofi da halaye da ake son gani da wadanda za su iya zama ‘yan takara.

Ana sanar da wanda ya zama sabon Paparoma ne ta hanyar samun kaso 2/3 na kuri’un da manyan masu zaben su ka kada.

A bisa ka’idar cocin, duk wanda aka yi wa wankan tsarki na  ” Baptisma”zai iya zama paparoma,amma  kuma tun daga 1378 ba a zabi wanda bai kai mukamin “Cardinal” ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sabbin Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci: Nan Ba Da Jimawa Ba, ‘Yan Ta’adda Za Su Ɗanɗana Kuɗarsu – COAS
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna
  •  Manyan Malaman Roman Katolika Sun Fara Taron Zabar Paparoma
  •  Bom Da Ya Tashi A Arewa Maso Gabashin Najeriya Ya Kashe Mutane 6
  • Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana
  • ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Mutum 8 Da Bam A Borno
  • Tawagar Jami’ai Da ‘Yan Kasuwar Ta Tunusiya Ta Gana Da Mataimakin Shugaban kasar Iran
  • Akwai Ƙarin Gishiri A Yawan  Masu Sauyin Jam’iyya Zuwa APC – El-Rufai
  • Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi
  • Ma’aikata 240 na karɓar albashi biyu, wasu 217 na amfani da lambar BVN ɗaya a Kano