Amurka Tace A Shirye Take Ta Shiga Yaki Da China
Published: 6th, March 2025 GMT
Shugaban ma’aikatan Tsaron kasar Amurka ko Pentagon Pete Hegseth ya bayyana cewa Amurka a shirye take ta shiga yaki da China, bayan da Beijing ta tabbatar da cewa zata tunkari kasar Amurka da dukkan karfinta kan ko ta ina ta fito mana a adawar da take nunawa kasar.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Hegseth yana fadar haka a jiya Laraba a lokacinda yake hira da shirin labarai na tashar talabijin ta Foxnews na Amurka.
Seketarin tsaron tsaron ya kara da cewa dok wanda yake son zaman lafiya to ya shiryawa yaki. Don haka kasar Amurka, inji Hegseth dole ta tabbatar da tana da sojojin masu karfi da makamai masu inganci don shiriwa ko ta kwana, saboda irin yadda kasar China take samun ci gaba mai yawa a bangaren tsaron kasarta.
Yace kasar China tana son ta maye gurbin Amurka a wurare da dama a duniya. Wanda hakan barazana ce gareta.
Yace ‘muna bukatar kashe kudade wa harkokin tsaro, wadanda suka hada makamai na zamani, don ganin yankin Ido-pecific ya ci gaba da zama karkashin ikon sojojin Amurka..
Jawaban da Hegseth na zuwa ne bayan da kasar china ta bayyana anniyarta na fuskantar dukkan barazanar da Amurka zata yiwa kasar, ta kara kudin fito da kasuwanci da sauransu, duk ta inda ta fito a shirye muke mu fuskanceta.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ambaliya ta yi ajalin mutum 30 a China
Ambaliya sanadiyyar wani mamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya ta yi ajalin mutane 30 a Arewacin China, lamarin da ya tilasta kwashe mutane fiye da 80,000 zuwa Beijing, babban birnin kasar.
Jaridar Beijing Daily ta ruwaito cewa ruwan saman ya haddasa rufe hanyoyi da dama da kuma katsewar lantarki a kauyuka sama da 130 yayin da jami’an agaji ke ci gaba da aikin ceto.
Jami’ar Jihar Gombe za ta fara sabbin darussa 6 a fannin noma ’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a sabon hari a AlkaleriA jiya Litinin ce Shugaban China, Xi Jinping ya ba da umarnin daukar matakan gaggauwa a yankunan da ke fuskantar hadarin ambaliya sakamakon mamakon ruwan da ake hasashen za a ci gaba da tafkawa.
Xi Jimping ya bukaci mahukuntan yankunan da ke fuskantar hadarin ambaliyar da su gaggauta samar da tsare-tsare domin kubutar da jama’a.
A yanzu haka ana hasashen samun saukar mamakon ruwan sama har zuwa gobe Laraba a wasu yankuna sama da 10 na China.
Tuni dai mahukunta suka sanar da bayar da tallafin kudi yuan miliyan 550 — kwatankwacin dalar Amurka miliyan 76.7 ga yankunan da ambaliyar ruwa ta shafa.
Gwamnatin kasar ta ce ta ware yuan miliyan 200 — kwatankwacin dalar Amurka miliyan 27.86 musamman ga birnin Beijing, inda ruwan sama kamar da bakin kwarya ya kashe akalla mutane 30 tare da haddasa barna mai yawa.
Bayanai sun ce ambaliyar ruwan ta kuma shafi lardunan Hebei, da Liaoning, da kuma Shandong, lamarin da ya haifar da asara mai yawa da asarar dukiya.