Jakadan JMI a hukumar makamashin Nukliya Mohsen Naziri ya bayyana cewa sabbin takurawar da kasashen yamma, musamman Amurka suke wa kasarsa ba zasu yi tasiri ba. Banda hakan zasu cutar da wadanda suka dora mana su,

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Naziri yana fadar haka a Jawabin da ya gabatar  a taron gwamnoni hukumar ta IAEA a birnin Geneva a jiya Laraba.

Ya ce kasashen yamma ne suka jagoranci karin takunkuman tattalin arziki a kan Iran, ko kuma bayyana cewa Iran bata bada hadin kai da ta dace ga hukumar makamashin Nukliya ta duniya wato IAEA. Da kuma zargin kasar Iran da cewa tana kokarin mallakan makaman Nukliya.

Naziri ya zargin kasashne yamma kan rashin cika al-kawalin da suka dauka a yarjeniyar JCPOA na shekara ta 2015, inda Amurka ta fara da janyewa daga yerjeniyar da aka dauki shekaru biyu cur ana tattaunawa a kanta.

Yace Amurka ta fice daga yaerjeniyar a shekara ta 2018 da sunan shi ne yarjeniya mafi muni wanda Amurka ta taba sanyawa hannu, kuma zata tilastwa Iran amincewa da sabuwar yarjeniya da ita, ko kuma ta sha wahala, ko gwamnatin JMI ta rushe karkashin takurawar ta.

Banda haka kasashen Turai wadanda suke goyon bayan Amurka sun ki cika nasu alkawulan a cikin yarjeniyar ta JCPOA.

Naziri Asl ya bayyana cewa martanin da Iran ta mayar shi ne, rage abinda yah au kanta a yarjeniyar, , wanda ita kanta Yarjeniyar ta bada damar yin haka a duk lokacinda dayan bangaren ya saba alkawulan da ta dauka a cikinta.

Ka’ida ta 26 da 36 na yarjeniyar ta bawa Iran wannan damar, na sabawa yarjeniyar don dawo da dayan bangaren kan abinda yakamata ya yi.

Ya kuma kara da cewa kasashen yamma basu da damar sake maida takunkuman tattalin arziki kan Iran saboda sune suka sabawa yarjeniyar.

Daga karshe ya ce Iran zata koma kan amfani da yarjeniyar ne kawai idan kasashen yamma sun dauke mata dukkan takunkuma tattalin arzikin da suka dora mata.

Sannan yace kasashen Ingila Faransa da Jamus sun sabawa kudurin kwamitin tsaro na MDD mai lamba 2231 wanda yake goyon bayan JCPOA.

Daga karshe yayi kira da gwamnonin hukumar ta IAEA da su maida hankalinsu wajen dabbaka kudurin na 2231.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasashen yamma a yarjeniyar

এছাড়াও পড়ুন:

 Iran Za Ta Kara Yawan Sanadarin Urani’um Da Take Tacewa A Wuri Na Sirri

A wani bayani na hadin gwiwa da hukumar makamashin Nukiliya ta Iran da kuma ma’aikatar harkokin wajen Iran su ka fitar, sun bayar da umarnin a bude wani wuri na daban na sirri domin ci gaba da tace sanadarin Urani’um, sannan kuma a maye gurbin bututu tace sanadarin mai  mataki na daya, da mai mataki na shida a cibiyar “Pardo.”

Bayanin dai ya zo ne a matsayin mayar da martani ga sanarwar da ta fito daga kwamitin alkalai na hukumar makamashin Nukiliya ta kasa da kasa akan Iran.

Bugu da kari, bayanin na Iran ya kuma ce; A kodayaushe jamhuriyar musulunci ta Iran tana aiki da nauyin da ya rataya a wuyanta, kuma har ya zuwa yanzu babu wani rahoto na hukumar wanda ya bayyana cewa; Iran ba ta aiki da ka’idojin hana yaduwar makaman Nukiliya.”

Haka nan kuma bayanin ya ambaci cewa; Tare da cewa Iran tana daukar rahoton da cewa na siyasa ne, wanda Amurka da kasashen turai suke amfani da hukumar a matsayin makami, ba tare da dogaro da wani dalili na ilimi ba.

Har ila yau Iran din ta zargi Amurka da kasashen na turai da wuce gona da iri wajen tsara rahoton da yake cin karo da rahoton da shugaban hukumar ta makamashin Nukiliya ya fitar, wanda bai sami wani abu mai  shiga duhu ba a cikin Shirin na Iran na zama lafiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wakilin Sin A IAEA Ya Yi Tir Da Harin Isra’ila Kan Cibiyoyin Sarrafa Nukiliyar Iran
  • Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Shaida Gamsuwa Da Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
  • Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin
  • Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka
  • An Kaddamar Da Bikin Gabatar Da Jerin Shirye-shiryen Telebijin Da Fina-finai Na CMG A Birnin Astana
  • Iran ta caccaki kudurin IAEA wanda ta ce yana cike da siyasa
  •  Iran Za Ta Kara Yawan Sanadarin Urani’um Da Take Tacewa A Wuri Na Sirri
  • Iran ta Yi Gargadin Cewa Zata Fice Daga Yarjeniyar NPT Idan Hukumar IAEA Ta Tir Da Ita
  • Kasashen Iran Masar Da Kuma Omman Sun Gudanar Da Taro A Oslo
  • Ministan man Fetur na Kasar Iran Yace Amurka Ta Kasa Hana Iran Saida Danyen Man Fetur Na Kasar