Jakadan JMI a hukumar makamashin Nukliya Mohsen Naziri ya bayyana cewa sabbin takurawar da kasashen yamma, musamman Amurka suke wa kasarsa ba zasu yi tasiri ba. Banda hakan zasu cutar da wadanda suka dora mana su,

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Naziri yana fadar haka a Jawabin da ya gabatar  a taron gwamnoni hukumar ta IAEA a birnin Geneva a jiya Laraba.

Ya ce kasashen yamma ne suka jagoranci karin takunkuman tattalin arziki a kan Iran, ko kuma bayyana cewa Iran bata bada hadin kai da ta dace ga hukumar makamashin Nukliya ta duniya wato IAEA. Da kuma zargin kasar Iran da cewa tana kokarin mallakan makaman Nukliya.

Naziri ya zargin kasashne yamma kan rashin cika al-kawalin da suka dauka a yarjeniyar JCPOA na shekara ta 2015, inda Amurka ta fara da janyewa daga yerjeniyar da aka dauki shekaru biyu cur ana tattaunawa a kanta.

Yace Amurka ta fice daga yaerjeniyar a shekara ta 2018 da sunan shi ne yarjeniya mafi muni wanda Amurka ta taba sanyawa hannu, kuma zata tilastwa Iran amincewa da sabuwar yarjeniya da ita, ko kuma ta sha wahala, ko gwamnatin JMI ta rushe karkashin takurawar ta.

Banda haka kasashen Turai wadanda suke goyon bayan Amurka sun ki cika nasu alkawulan a cikin yarjeniyar ta JCPOA.

Naziri Asl ya bayyana cewa martanin da Iran ta mayar shi ne, rage abinda yah au kanta a yarjeniyar, , wanda ita kanta Yarjeniyar ta bada damar yin haka a duk lokacinda dayan bangaren ya saba alkawulan da ta dauka a cikinta.

Ka’ida ta 26 da 36 na yarjeniyar ta bawa Iran wannan damar, na sabawa yarjeniyar don dawo da dayan bangaren kan abinda yakamata ya yi.

Ya kuma kara da cewa kasashen yamma basu da damar sake maida takunkuman tattalin arziki kan Iran saboda sune suka sabawa yarjeniyar.

Daga karshe ya ce Iran zata koma kan amfani da yarjeniyar ne kawai idan kasashen yamma sun dauke mata dukkan takunkuma tattalin arzikin da suka dora mata.

Sannan yace kasashen Ingila Faransa da Jamus sun sabawa kudurin kwamitin tsaro na MDD mai lamba 2231 wanda yake goyon bayan JCPOA.

Daga karshe yayi kira da gwamnonin hukumar ta IAEA da su maida hankalinsu wajen dabbaka kudurin na 2231.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasashen yamma a yarjeniyar

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka ta sake laftawa wasu kamfaninin mai na Iran takunkumi

Amurka ta sanar da kakaba takunkumi kan wasu kamfanoni 7 da ta ce suna da hannu wajen siyar da man kasar Iran, a wani mataki na kara matsin lamba duk da tattaunawar da aka yi kan shirin nukiliyar Iran.

Sanarwar da ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta fitar ta ce, bangarorion da takunkumin ya shafa sun hada da kamfanonin kasuwanci guda biyar, hudu da ke Hadaddiyar Daular Larabawa, daya kuma a kasar Turkiyya, wadanda suka sayar da albarkatun man fetur na kasar Iran ga kasashe uku, da kuma wasu kamfanonin jigilar kayayyaki guda biyu.

A cikin sanarwar da sakataren harkokin wajen kasar ta Amurka Marco Rubio ya fitar, ya ce “Matukar dai Iran na son samar da kudaden shiga na man fetur da sinadarai don samar da kudaden gudanar da ayyukanta na tabarbarewar zaman lafiya, da kungiyoyin da ya bayyana da na ta’addanci to Amurka za ta dauki matakin laftawa Iran da dukkan kawayenta alhakin kaucewa takunkumi.”

Matakin na zuwa ne jim kadan bayan Iran ta sanar da cewa za a sake gudanar da zagaye na hudu na tattaunawa da gwamnatin shugaba Donald Trump a birnin Rome a ranar Asabar 3 ga watan Mayu a karkashin jagorancin kasra Oman.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
  • Iran ta sha alwashin ci gaba da aiwatar da manufofinta na raya dangantakarta da Nijar
  • Amurka ta sake laftawa wasu kamfaninin mai na Iran takunkumi
  • Iran Da Iraki Sun Ce An Kammala Shimfida Layin Dogo Daga Shalamcheh Zuwa Basra
  • Xi Jinping Ya Ziyarci Sabon Bankin Raya Kasashen BRICS
  • Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
  • Shin Amurka Na Iya Komawa Kan Kadaminta A Matsayin Cibiyar Masana’antun Duniya?
  • Shugaban Kasar Yana Maraba Da Masu Zuba Hannun Jari A Kasarsa Daga Kasashen Waje
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Tattauana Da Shugaban Hukumar IAEA
  • Iran Da Rasha Sun Jaddada Yin Aiki Tare A Fagen Kiwon Lafiya