Mutanen Afrika Sun Kori Kasar Faransa Daga Kashensu Ne Saboda Ta Ki Ta Amince Da Yencinsu
Published: 6th, March 2025 GMT
Pierre de Gaulle, dan tsohon shugaban kasar Faransa Charles de Gaulle, wanda ya jagoranci kasar Faransa a samun yencin kasar daga hannun sojojin NAZi a yakin duniya na biyu, ya bayyana cewa kasashen Afrika sun kore kasar Faransa daga kasashensu ne bayan da kasar ta kasa yin abinda zai kawo ci gaban kasashen.
Kamfanin dillancin labaran Spunik na kasar Rasha ya nakalto jikan de Gaulle yace tsarin kasar Faransa na tattalin arziki da siyasa sun sanya kasashen cikin talauci da rashin ci gaba. Wannan ya sa suka zabi korar kasar Faransa daga kasashensu.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Faransa
এছাড়াও পড়ুন:
An Fara Baje Kolin Kayakin Da Ake Kerawa A Iran Tare Da Taron Iran Da Afirka Karo Na Uku
An fara kasuwar baje koli na kayakin kasuwancin da ake samarwa a cikin Iran ko IRAN EXPO 2025, karo na 3 a nan Tehran.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa kasuwar baje koli na Iran EXPO 2025 zai jawa masu zuna jari daga kasashen Afirka.
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya fadawa kamfanin dillancin labaran IP kan cewa Kasuwar ta bana dai, za ta tara kamfanonin masu samar da kayaki daga yankuna daban daban na kasar Iran da dama, kuma akwai fatan cewa wannan kasuwar ta zama mabudi ga kyautatuwan tattalin arzikin kasar.
EXPO dai ita ce kasuwar baje koli na kayakin kasar Iran mafi girma wanda ake gudanarwa a ko wace shekara, sannan daga nan take samun kasuwa a kasashen duniya. Kuma yan kasuwa daga kasahe fiya da 100 ne suka shigo kasar don halattan kasuwar.
Esma’il Bakaee, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya ce ya na fatan a wannan kasuwar, kasashen Afirka da Iran za su amfani juna a harkokin kasuwancin da ake bunkasa a tsakaninsu.