Majiyar Fadar Shugaban Kasar Amurka Tace Ta Shiga Tattaunawa Kai Tsaye Da Kungiyar Hamas A Gaza
Published: 6th, March 2025 GMT
Sakataren watsa labarai na Fadar white House ta tabbatar da cewa gwamnatin Amurka ta shiga tattaunawa da kungiyar Hamas wacce take iko da zirin Gaza kai tsaye.
Tashar talabijin ta Presstv a nann Tehran ta nakalto Karoline Leavitt tana fadar haka a jiya Laraba, ta kuma kara da cewa, shugaban kasar Amurka Donal Trump ya aiki Adam Boehler mutumin da yake wakiltansa a al-amuran fursinonin Amurka a waje, zuwa kasashen yankin kudancin Asiya don tattauna batun Amurkawa da suke hannun kungiyar Hamas a Zirin Gaza.
Leavitt ta kara da cewa Amurkawa sun cancanci a shiga tattaunawa ko kuma a bi duk hanyoyin da suka dace don ganin, an kubutar da Amurka wadanda suka shiga hanun makiyansu a ko ina suke a duniya.
Wannan labarin yana zuwa ne a lokacinda fadar ta white hause ta bayyana kungiyar Hamas a matsayin kungiyar yan ta’adda.
Hamas ta fara kama Amurkawa ta tsare tun shekara 1997 bayan da Amurka ta fito fili tana goyon bayan HKI kan kisan kiyashin da takewa Falasdinawa a Gaza da sauran wurare.
Rahoton ya kara da cewa Amurka ta fara tattaunawa da kungiyar ne a birnin Doha na kasar Qatar a cikin yan makonnin da suka gabata.
A halin yanzu dai Hamas tana rike da fursinoni 59 daga cikin 240 da suka kama a ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kungiyar Hamas
এছাড়াও পড়ুন:
Jiragen Yakin Amurka Sun Kashe Mutane Da Dama A lardin Sa’ada Na Kasar Yemen
Mutane da dama daga nahiyar Afirka ne suke cikin mutane kimani 50 wadanda suka rasa rayukansu sanadiyyar hare-haren da jiragen yakin Amurka suka kai kan wani gidan kaso a lardin Sa’ada na kasar Yemen.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kamfanin dillancin labaran Al-Masirah yana cewa makaman Amurka sun fada kan wani gidan yarin da aka kebewa yan Afrika, kuma yawansu ya kai 115, amma har yanzun ba’a san yawan wadanda suka rasa rayukansu a gidan yari.
Labarin ya kara da cewa har yanzun ma’aikatan agaji suna aikin ceto a wurin, sannan hotunan da suka fara bayyana sun nuna gawaki da dama. Amma Al-Masirah ta bayyana cewa akalla mutane 68 sun rasa rayukansu.