Gwamna Mallam Umar Namadi na jihar Jigawa ya karbi lasisin yin hada hadar kasuwanci na kasa da kasa, wato kasuwanci maras shinge a kan iyakar  Maigatari a hukumance, wanda hukumar kula da sarrafa kayayyaki ta Najeriya NEPZA ta bayar kwanan nan.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da babban sakataren yada labaran gwamnan Hamisu Mohammed Gumel ya rabawa manema labarai a Dutse.

Ya bayyana cewa, kwamishinan kasuwanci, da masana’antu, Alhaji Aminu Kanta ne ya mika wa Gwamna Umar Namadi lasisin a ofishinsa.

Hamisu Mohammed Gumel ya bayyana cewa, tun lokacin da aka kafa wannan gwamnati mai ci ta dukufa wajen gudanar da aikin karbar lasisin aikin daga NEPZA

A cewarsa, wannan ya nuna karara da kudurin gwamnati na bunkasa tattalin arziki, da inganta harkokin kasuwanci, da kuma sanya jihar Jigawa a matsayin babbar cibiyar zuba jari da bunkasa masana’antu.

Sakataren yada labaran ya yi nuni da cewa, kafa harkar cinikayya a kan iyakar Maigatari na da nufin jawo hankalin masu zuba jari na gida da waje, da inganta samar da ayyukan yi, da bunkasa harkokin kasuwanci, musamman a yankin arewacin Najeriya.

Ya ce, Gwamna Namadi ya nuna jin dadinsa ga kokarin hadin gwiwa da ya kai ga samun lasisin tare da jaddada aniyar gwamnatinsa na samar da yanayi mai kyau don gudanar da kasuwanci yadda ya kamata.

Hamisu ya yi nuni da cewa, a karkashin gwamnatin Gwamna Umar Namadi, wannan yunkuri ya samu gagarumin ci gaba da nufin bunkasa tattalin arziki da habaka masana’antu a jihar.

Kwamishinan ya samu rakiyar Kodineta na shiyyar kasuwanci maras shinge ta Maigatari, Abdulaziz Usman Abubakar da mai kula da shiyyar Bello Abdullahi Nura.

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutumin Da Ake Tuhuma Da Safarar Miyagun Kwayoyi

A kokarinsa na gano hakikanin dalilan da suka sa aka bayar da beli ga wani sanannen mai safarar miyagun kwayoyi, Sulaiman Aminu Dan Wawu, da aka ce an sako shi bisa umarnin Kwamishinan Sufuri na Kano, Ibrahim Ali Namadi, Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya kaddamar da wani kwamiti na mutum takwas domin gudanar da bincike mai zurfi.

Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Alhaji Umar Faruk Ibrahim ne ya kaddamar da kwamitin a madadin gwamnan.

An umurci kwamitin da ya gudanar da binciken cikin mako guda, domin gano hakikanin abin da ya faru da kuma ba da shawarwari kan matakin da ya dace a dauka.

Shugaban kwamitin shi ne Mai Bai wa Gwamna Shawara kan Harkokin Shari’a da Dokoki, Barista Aminu Hussaini, yayin da Mambobin kwamitin suka hada da Barista Hamza Haladu, Barista Hamza Nuhu Dantani, Darakta Janar na Hukumar Ayyuka na Musamman, Manjo Janar Muhammad Sani (rtd), Comrade Kabiru Dakata, da Farfesa Mamun Mustapha daga Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Dangote da ke Wudil.

Sauran mambobin sun hada da Alhaji Abdullahi Mahmud Umar, Kwamishina II na Hukumar Kula da Ma’aikata, da Hajiya Bilkisu Shehu Mai Mota, Babbar Sakatariya a Sashen Gudanarwa da Sauran Ayyuka na  ofishin Sakataren Gwamnatin .Jihar, wadda za ta rike matsayin Sakatariya ga kwamitin.

Gwamna Yusuf ya bayyana damuwarsa matuka kan zargin da ake yi, inda ya sake jaddada kudirinsa na yaki da safarar miyagun kwayoyi da duk wani nau’in barna a cikin al’umma.

Sakataren Gwamnatin Jihar ya bayyana kwarin gwiwarsa kan mambobin kwamitin, yana mai cewa an zabo su ne bisa cancanta, kwarewa, karsashi, da kuma kwarin gwiwar cewa za su gudanar da wannan aiki yadda ya kamata.

 

Abdullahi Jalaluddeen

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Tallafin Miliyoyin Naira Ga Ƴan NURTW da Mahauta a Jigawa
  • Shugabannin Arewa Sun Tattauna Sabon Hanyar Ci Gaba – Minista Uba Maigari Ya Yaba
  • Kasashen Yankin Caribbean Suna Son Bunkasa Alakarsu Ta Kasuwanci Da Nahiyar Afirka
  • Gwamna Namadi Ya Naɗa Shugabannin Hukumar Hisbah Ta Jihar Jigawa
  • Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • Babu Wata Karamar Hukumar Dake Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • Gwamna Lawal Ya Naɗa Sabon Sarkin Gusau
  • Gwamna Namadi Ya Biya Sama Da Naira Biliyan Daya Ga Tsofaffin Ma’aikata
  • Mutum miliyan 1.2 na fama da ciwon hanta a Kano
  • Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutumin Da Ake Tuhuma Da Safarar Miyagun Kwayoyi