Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-03@04:00:48 GMT

Jigawa Ta Kebe Wuraren 57 don Kare Rikicin Manoma da Makiyaya

Published: 28th, February 2025 GMT

Jigawa Ta Kebe Wuraren 57 don Kare Rikicin Manoma da Makiyaya

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce daga cikin wuraren kiwo guda 400 da ke jihar, ta duba 57 domin dakile rikicin manoma da makiyaya a jihar.

 

Gwamna Umar Namadi ya bayyana haka ne a wajen bude taron tuntubar masu ruwa da tsaki kan sauye-sauyen kiwo tare da hadin gwiwa da kwamitin shugaban kasa na aiwatar da gyara harkokin kiwon dabbobi da aka gudanar a Dutse, babban birnin jihar.

 

Ya ce baya ga samar da tsarin doka na kare wuraren kiwo, manufar za ta kuma tabbatar da amfani da albarkatun kasa mai dorewa a jihar.

 

Gwamnan ya ce gwamnatin sa ta kuma dauki ma’aikatan kiwon lafiyar dabbobi 300 na al’umma domin su samar da ayyukan ci gaba ga manoma domin inganta harkar noma a jihar.

 

“Mun dauki aiki tare da horar da ma’aikatan kula da lafiyar dabbobi 300 na al’umma don gudanar da asibitocin kula da dabbobi ta wayar hannu guda 300 a fadin jihar kuma kawo yanzu ra’ayoyin da aka bayar kan hakan ya gamsar da su.

 

“Mun kuma yi wa dabbobi sama da dubu 560 allurar rigakafi a karkashin shirinmu na rigakafi na yau da kullun, muna ba su kariya daga cututtuka da kuma inganta sana’arsu.

 

“Wannan matakin ba wai kawai ya inganta kiwon dabbobi ba, har ma ya kara samar da kudin shiga ga manoman mu ta yadda kiyon dabbobi ya dore,” in ji Gwamnan.

 

Ya yi nuni da cewa ayyukan da gwamnatin jihar ke yi a fannin kiwo na ci gaba da samun sakamako mai kyau a kudurin kawo sauyi da inganta tasirinsa ga tattalin arzikin jihar.

 

“Yayin da muke shirin samar da ingantaccen tsari mai inganci na Kiwo ga Jiha, abin farin ciki ne a lura cewa ayyukan da muka yi a fannin kiwo sun ci gaba da samun sakamako mai kyau.

 

Namadi ya jaddada cewa, “Labarin nasarorin da muka samu wajen kafa ginshikin ci gaba mai dorewa sun hada da karfafa hanyoyin ganowa da wuri, da sassautawa da warware rikicin manoma da makiyaya tare da mai da hankali kan wuraren da ake samun matsala a tarihi,” Namadi ya jaddada.

 

Malam Umar Namadi ya yi alkawarin dorewar hadin gwiwa tsakanin hukumar manoma da makiyaya ta jihar Jigawa da kwamitin tsaro na masu ruwa da tsaki a bangarori da dama domin wanzar da zaman lafiya tsakanin manoma da makiyaya domin dorewar samar da ci gaba a fannin kiwo.

 

KARSHE/USMAN MZ

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa manoma da makiyaya

এছাড়াও পড়ুন:

An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi

’Yan bindiga sun sace Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kebbi, Honarabul Samaila Bagudu, a garinsu da ke Ƙaramar Hukumar Bagudu.

Rahotanni sun bayyana cewa ’yan bindigar sun mamaye garin Bagudu ne da yammacin ranar Juma’a tare da yin harbe-harbe don tsorata al’umma.

Maharan sun yi awon gaba da ɗan majalisar ne a kan hanyarsa ta dawowa daga masallaci bayan ya an idar da sallah masallaci a garin na Bagudu.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Babban Sakataren Yaɗa Labarai na Gwamnatin Jihar Kebbi, Ahmed Idris, ya ce an sanar da hukumomin tsaro, kuma ana ci gaba da ƙoƙarin tabbatar da kuɓutar da Mataimakin Shugaban Majalisar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya
  • Rikicin PDP: Tsagin Wike ya dakatar da Damagum
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi
  • Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma