Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-09-18@05:43:54 GMT

Jigawa Ta Kebe Wuraren 57 don Kare Rikicin Manoma da Makiyaya

Published: 28th, February 2025 GMT

Jigawa Ta Kebe Wuraren 57 don Kare Rikicin Manoma da Makiyaya

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce daga cikin wuraren kiwo guda 400 da ke jihar, ta duba 57 domin dakile rikicin manoma da makiyaya a jihar.

 

Gwamna Umar Namadi ya bayyana haka ne a wajen bude taron tuntubar masu ruwa da tsaki kan sauye-sauyen kiwo tare da hadin gwiwa da kwamitin shugaban kasa na aiwatar da gyara harkokin kiwon dabbobi da aka gudanar a Dutse, babban birnin jihar.

 

Ya ce baya ga samar da tsarin doka na kare wuraren kiwo, manufar za ta kuma tabbatar da amfani da albarkatun kasa mai dorewa a jihar.

 

Gwamnan ya ce gwamnatin sa ta kuma dauki ma’aikatan kiwon lafiyar dabbobi 300 na al’umma domin su samar da ayyukan ci gaba ga manoma domin inganta harkar noma a jihar.

 

“Mun dauki aiki tare da horar da ma’aikatan kula da lafiyar dabbobi 300 na al’umma don gudanar da asibitocin kula da dabbobi ta wayar hannu guda 300 a fadin jihar kuma kawo yanzu ra’ayoyin da aka bayar kan hakan ya gamsar da su.

 

“Mun kuma yi wa dabbobi sama da dubu 560 allurar rigakafi a karkashin shirinmu na rigakafi na yau da kullun, muna ba su kariya daga cututtuka da kuma inganta sana’arsu.

 

“Wannan matakin ba wai kawai ya inganta kiwon dabbobi ba, har ma ya kara samar da kudin shiga ga manoman mu ta yadda kiyon dabbobi ya dore,” in ji Gwamnan.

 

Ya yi nuni da cewa ayyukan da gwamnatin jihar ke yi a fannin kiwo na ci gaba da samun sakamako mai kyau a kudurin kawo sauyi da inganta tasirinsa ga tattalin arzikin jihar.

 

“Yayin da muke shirin samar da ingantaccen tsari mai inganci na Kiwo ga Jiha, abin farin ciki ne a lura cewa ayyukan da muka yi a fannin kiwo sun ci gaba da samun sakamako mai kyau.

 

Namadi ya jaddada cewa, “Labarin nasarorin da muka samu wajen kafa ginshikin ci gaba mai dorewa sun hada da karfafa hanyoyin ganowa da wuri, da sassautawa da warware rikicin manoma da makiyaya tare da mai da hankali kan wuraren da ake samun matsala a tarihi,” Namadi ya jaddada.

 

Malam Umar Namadi ya yi alkawarin dorewar hadin gwiwa tsakanin hukumar manoma da makiyaya ta jihar Jigawa da kwamitin tsaro na masu ruwa da tsaki a bangarori da dama domin wanzar da zaman lafiya tsakanin manoma da makiyaya domin dorewar samar da ci gaba a fannin kiwo.

 

KARSHE/USMAN MZ

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa manoma da makiyaya

এছাড়াও পড়ুন:

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

Ofishin yada labarai na majalisar gudanarwar Sin ya gudanar da taron manema labarai da misalin karfe 10 na safiyar yau Litinin, inda kakakin hukumar kididdiga ta kasar, kuma babban masanin tattalin arziki, kana daraktan sashen kididdigar tattalin arziki na kasar, Fu Linghui ya yi karin haske kan ayyukan tattalin arzikin kasar cikin watan Agustan bana, tare da amsa tambayoyin manema labarai.

A cewar bayanan da aka gabatar a yayin taron, ayyukan tattalin arzikin kasar a watan Agusta sun samu ci gaba ba tare da tangarda ba. Kuma hakan ya bayyana ne ta hanyoyi daban-daban kamar haka: masana’antu sun habaka cikin sauri, masana’antar kera kayayyakin aiki da masana’antar fasaha sun samu ci gaba mai kyau. Kana ayyukan bayar da hidima su ma sun bunkasa cikin sauri. Baya ga haka, an samu ci gaba mai kyau a bangaren bayar da hidimomi na zamani. Harkokin kasuwanci sun samu ci gaba cikin natsuwa, inda harkokin sayar da kayayyaki ga masu sayayya suka kara habaka. Har ila yau, kadarorin jari sun ci gaba da karuwa, jarin masana’antu ya habaka cikin sauri, harkokin fice da shigen kayayyaki sun ci gaba da girma, tsarin kasuwanci ya ci gaba da ingantuwa, kana yanayin samar da guraben aikin yi, ya kasance kan wani mataki mai daidaito. Sai dai kuma saboda yanayin da ake ciki, adadin marasa aikin yi a birane ya karu, ma’aunin Core CPI ya ci gaba da hauhawa, kana faduwar farashin kayayyakin masana’antu ya ragu.

Bayanan sun kara da cewa, akwai bukatar lura da cewa, ana fuskantar yanayin rashin tabbas a waje, kuma tattalin arzikin kasar Sin yana fuskantar kalubale da hadari da yawa. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kammala Ziyarar Yini 3 A Ma’aikatar Kananan Hukumomin Jihar
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
  • Kungiyar Kare Hakkokin Bil’Adama Ta Siriya Ta Bankado Karin Fararen Hula Da Aka Kashe A Rikicin Suweida
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta