Hukumar Tsaro Ta Farin Kaya Ta Kama Wasu Mutane 2 Da Yin Sojan Gona
Published: 24th, February 2025 GMT
Hukumar tsaro ta farin kaya (NSCDC) reshen jihar Kano ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da yin sojan gona ga aikin hukumar.
Jami’in hulda da jama’a na hukumar NSCDC reshen jihar Kano SC Ibrahim Idris Abdullahi ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Kano.
Ya ce mutanen biyu, Muhammad Sarari da Madaki Zaharaddeen, masu shekaru 43 da 32, mazauna Goron Dutse ne, a karamar hukumar Dala, da Hotoro kwatas a karamar hukumar Nassarawa.
A cewar jami’in hulda da jama’an, wadanda ake zargin suna zuwa hukumomin da ma’aikatun gwamnati ne, inda suke yaudarar manyan ma’aikata tare karbar kudade daga hannunsu.
“Dubunsu ta cika ne a lokacin da suka yi yunkurin tsoratar da wasu manyan ma’aikatan gidan talabijin na jihar, suna neman su basu wasu kudade.” In ji shi.
Jami’an hukumar ta NSCDC reshen Tarauni ne suka kama wadanda ake zargin, inda aka kawo su hedikwatar jihar domin yi musu tambayoyi.
Da aka gudanar da bincike, sun amince da aikata laifin, kuma an sami daya daga cikinsu da katin shaida na bogi da rigar ciki mai dauke da tambarin hukumar NSCDC.
Ya kuma yi nuni da cewa, za a tuhumi wadanda ake zargin ne da laifin shiga harkar aikin gwamnati, da hada baki, da tsoratarwa, da kuma karbar kudi.
Abdullahi ya kara da cewa hukumar NSCDC reshen jihar Kano ta kammala bincikenta, za kuma kuma a kaisu gaban kotu.
Abdullahi Jalaluddeen
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Amurka ta sake laftawa wasu kamfaninin mai na Iran takunkumi
Amurka ta sanar da kakaba takunkumi kan wasu kamfanoni 7 da ta ce suna da hannu wajen siyar da man kasar Iran, a wani mataki na kara matsin lamba duk da tattaunawar da aka yi kan shirin nukiliyar Iran.
Sanarwar da ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta fitar ta ce, bangarorion da takunkumin ya shafa sun hada da kamfanonin kasuwanci guda biyar, hudu da ke Hadaddiyar Daular Larabawa, daya kuma a kasar Turkiyya, wadanda suka sayar da albarkatun man fetur na kasar Iran ga kasashe uku, da kuma wasu kamfanonin jigilar kayayyaki guda biyu.
A cikin sanarwar da sakataren harkokin wajen kasar ta Amurka Marco Rubio ya fitar, ya ce “Matukar dai Iran na son samar da kudaden shiga na man fetur da sinadarai don samar da kudaden gudanar da ayyukanta na tabarbarewar zaman lafiya, da kungiyoyin da ya bayyana da na ta’addanci to Amurka za ta dauki matakin laftawa Iran da dukkan kawayenta alhakin kaucewa takunkumi.”
Matakin na zuwa ne jim kadan bayan Iran ta sanar da cewa za a sake gudanar da zagaye na hudu na tattaunawa da gwamnatin shugaba Donald Trump a birnin Rome a ranar Asabar 3 ga watan Mayu a karkashin jagorancin kasra Oman.