Hukumar tsaro ta farin kaya  (NSCDC) reshen jihar Kano ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da yin sojan gona ga aikin hukumar.

Jami’in hulda da jama’a na hukumar NSCDC reshen jihar Kano SC Ibrahim Idris Abdullahi ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Kano.

Ya ce mutanen biyu, Muhammad Sarari da Madaki Zaharaddeen,   masu shekaru 43 da 32, mazauna Goron Dutse ne, a karamar hukumar Dala, da Hotoro kwatas a karamar hukumar Nassarawa.

A cewar jami’in hulda da jama’an, wadanda ake zargin suna zuwa hukumomin da ma’aikatun gwamnati ne, inda suke yaudarar manyan ma’aikata tare karbar kudade daga hannunsu.

“Dubunsu ta cika ne a lokacin da suka yi yunkurin tsoratar da wasu manyan ma’aikatan gidan talabijin na jihar, suna neman su basu wasu kudade.” In ji shi.

Jami’an hukumar ta NSCDC reshen Tarauni ne suka kama wadanda ake zargin, inda aka kawo su hedikwatar jihar domin yi musu tambayoyi.

Da aka gudanar da bincike, sun amince da aikata laifin, kuma an sami daya daga cikinsu da katin shaida na bogi da rigar ciki mai dauke da tambarin hukumar NSCDC.

Ya kuma yi nuni da cewa, za a tuhumi wadanda ake zargin ne da laifin shiga harkar aikin gwamnati, da hada baki, da tsoratarwa, da kuma karbar kudi.

Abdullahi ya kara da cewa hukumar NSCDC reshen jihar Kano ta kammala bincikenta, za kuma kuma a kaisu gaban kotu.

 

Abdullahi Jalaluddeen

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Akwa Ibom

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Zulum Ya Sauke Kwamishinoni Biyu Tare Da Maye Gurbinsu Da Wasu
  • Mun yi asarar shanu 340 a hannun ɓarayi a Yuli — Miyetti Allah
  • ZAMFARA: APC Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Dauki Don Matsalar Tsaro Na Kara Tsananta
  • Kwara Ta Kwashe Mabarata Daga Titunan Jihar Su 94
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • Kwamitin Aikin Hajjin 2025 Na Jihar Kano Ya Kammala Rahoton Aikinsa Na Wucin Gadi
  • Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • Babu Wata Karamar Hukumar Dake Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • ‘Yan Sanda A Kano Sun Kama Kasurgumin Dan Fashin Nan Barga Da Wasu Mutum 14
  • EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Akwa Ibom