Jam’iyyar NNPP reshen jihar Kano ta dakatar da ‘yan majalisar tarayya huɗu bisa zargin aikata abubuwan da suka saɓa wa manufofin jam’iyya. Shugaban jam’iyyar a jihar, Alhaji Hashimu Dungurawa, ne ya bayyana hakan yayin da yake zantawa da manema labarai a Kano a ranar Litinin.

Waɗanda aka dakatar sun hada da Kawu Sumaila (Sanatan Kano ta Kudu), Ali Madakin Gini (Dala), Sani Rogo (Rogo/Karaye), da Kabiru Rurum (Rano/Kibiya).

Dungurawa ya ce waɗannan ‘yan majalisa sun samu tikitin NNPP ne, amma daga baya suka fara aikata abubuwan da suka sabawa jam’iyyar.

Nan Kusa Ƴan Majalisun NNPP Za Su Koma APC – Ganduje  Jam’iyyar NNPP Daya INEC Ta Amince Da Ita – Shugaban Jam’iyyar 

Ya ce misali, Sanata Sumaila ya ƙaddamar da wasu ayyuka a jami’arsa ba tare da ya gayyaci wakilan jam’iyyar ba, wanda hakan ya nuna alamun yi wa NNPP zagon ƙasa. Shugaban jam’iyyar ya ƙara da cewa za a kafa kwamitin bincike domin tantance lamarin da ɗaukar matakin da ya dace.

Sai dai Dungurawa ya ce har yanzu jam’iyyar na da shirin sasanta matsalar, inda ya bayyana cewa idan waɗanda aka dakatar suka gyara dangantakarsu da jam’iyya, za a iya dawo da su. Wannan matakin na zuwa ne a daidai lokacin da ake samun rahotannin rikicin cikin gida a NNPP, inda wasu mambobi ke kukan ana ware su daga harkokin jagoranci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

ACF ta mara wa gwamnatin Tinubu baya

Ƙungiyar Tuntuɓa ta Arewa (ACF), ta bayyana cikakken goyon bayanta ga gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da Mataimakinsa, Kashim Shettima.

Shugabannin ƙungiyar sun kai wa Mataimakin Shugaban Ƙasa, ziyara a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja, inda suka gayyace shi zuwa bikin cika shekaru 25 da kafa ACF.

An sanya dokar hana fita bayan ɓarkewar zanga-zanga kan zaɓen Tanzania Gwamnati ta bai wa ASUU N2.3bn domin biyan bashin albashin malamai

Shugaban kwamitin amintattu na ACF, Alhaji Bashir Dalhatu, ya yaba da kyakkyawar alaƙar aiki tsakanin Shugaba Tinubu da Shettima, ya bayyana cewa hakan alama ce ta haɗin kai da shugabanci na gari.

“A wajenmu ’yan Arewa, Mataimakin Shugaban Ƙasa shi ne jakadanmu na farko. Yana yin biyayya ga Shugaban Ƙasa kuma yana aiki tuƙuru ba don Arewa kaɗai ba, har ma da Najeriya gaba ɗaya,” in ji Dalhatu.

Dalhatu, ya ƙara da cewa ACF za ta ci gaba da mara wa gwamnati baya tare da ba ta shawarwari masu amfani a duk lokacin da ya dace.

“Muna alfahari da Mataimakin Shugaban Ƙasa da sauran ’ya’yanmu na Arewa da ke cikin gwamnati.

“Za mu ci gaba da goyon bayansu, amma kuma za mu nuna musu wuraren da ake buƙatar gyara domin amfanin dukkanin ’yan Najeriya,” in ji shi.

Ya bayyana cewa ACF, wadda aka kafa a shekara ta 2000, an samar da ita ne domin haɗa kan al’ummar Arewa da kuma ƙarfafa zaman lafiya da ci gaban ƙasa baki ɗaya.

A cewarsa, ƙungiyar ta taka muhimmiyar rawa wajen magance rikice-rikice, tallafa wa ci gaban tattalin arziƙi, da kuma ƙarfafa wa matasa da al’umma gwiwa su dogara da kansu ta hanyar ilimi da sana’o’i.

Dalhatu, ya ce bikin cikar ƙungiyar shekaru 25 da kafuwa, zai zama dama ta haɗa kan ƙasa, inda za su gayyaci manyan ƙungiyoyin yankuna kamar Afenifere, Ohanaeze Ndigbo da PANDEF domin ƙarfafa zumunci da fahimtar juna.

Hakazalika, ya yi fatan bikin zai taimaka wajen ƙarfafa haɗin kai da zaman lafiya a tsakanin ƙabilu Najeriya domin samun ci gaban ƙasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rikicin PDP: Tsagin Wike ya dakatar da Damagum
  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike
  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu da ke da alaƙa da Wike
  • Kotu ta dakatar da gudanar da babban taron PDP
  • Kotu ta dakatar da babban taron PDP na ƙasa
  • Kotu ta dakatar da babban taron PDP
  • An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku
  • Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure
  • ACF ta mara wa gwamnatin Tinubu baya