Aminiya:
2025-06-15@17:17:29 GMT

PDP ta lashe zaɓen ƙananan hukumomin Osun

Published: 22nd, February 2025 GMT

Jam’iyyar PDP mai ci a Jihar Osun ta lashe zaɓen dukkan kujerun ƙananan hukumomi jihar guda 30 da na kansiloli 332 da aka gudanar yau Asabar.

Shugaban hukumar zaɓen jihar OSSIEC, Hashim Abioye ne ya sanar da sakamakon a wani taron ganawa da manema labarai da ya yi a jihar.

Wani mutum ya yi wa agolarsa fyaɗe ta samu juna biyu An haifi alade mai fuskar mutum a Philippines

Da yake jawabi a yammacin wannan Asabar ɗin a birnin Osogbo, Hashim Abioye ya ce an samu nasarar gudanar da zaɓen bisa duk wasu tsare-tsare da dokoki suka tanadar.

Ya bayyana cewa jam’iyyu 18 ne suka shiga zaɓen domin cike giɓin da ake da shi a madafan iko na ƙananan hukumomin jihar guda 30.

Aminiya ta ruwaito cewa an samun takun saƙa tsakanin gwamnatin jihar da ’yan sanda da ma Ministan Shari’a na Nijeriya.

Ministan ya buƙaci a dakatar da zaɓen, sannan ’yan sanda suka ce sun samu bayanan sirri kan yiwuwar tayar da hargitsi, don haka suka yi kira ga gwamnan da ya dakatar da yunƙurinsa na gudanar da zaɓen, lamarin da shi kuma ya ce babu gudu, babu ja da baya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Osun Zaɓen Ƙananan Hukumomi

এছাড়াও পড়ুন:

An samu gobara a wasu matatun mai guda biyu na Iran bayan harin da Isra’ila ta kai

Wasu Hare-haren da gwamnatin Isra’ila ta kai ya haddasa gobara a wasu matatun mai a lardin Bushehr da ke kudancin kasar Iran.

Gobarar ta tashi ne a wurin a ranar Asabar bayan da wasu kananan jiragen yakin Isra’ila guda biyu suka kai hare-hare a kan kayayyakin sarrafa iskar gas da ke yankin kudancin Pars.

Hare-haren sun yi haddassa fashe fashe a matatar iskar gas ta Fajr-e Jam, daya daga cikin mafi girma a Iran, da kuma wata karamar matatar mai a mataki na 14 na tashar iskar gas ta Kudu Pars.

Har yanzu ba a fitar da kiyasin barnar a hukumance ba.

Bayan gobarar, ma’aikatar mai ta Iran ta fitar da wata sanarwa inda ta tabbatar da harin.

Sanarwar ta ce, nan da nan aka kaddamar da aikin shawo kan gobarar da dakile ta.”

Matatar man ta Pars ta kudu ita ce tashar iskar gas mafi girma a duniya, wacce ke kan iyakar teku tsakanin Iran da Qatar.

Ta kunshi sama da kashi 70% na bukatun iskar gas na Iran.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Harin Benuwe: ’Yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zanga
  • Oman ta tabbatar da soke tattaunawar Iran da Amurka zagaye na shida
  • An samu gobara a wasu matatun mai guda biyu na Iran bayan harin da Isra’ila ta kai
  • Trump ya dakatar da kamen baƙin haure a wasu wurare na Amurka
  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Miliyoyin Mutane Sun Gudanar  Da Bukukuwan “Idin Gadir” A Tehran Da Sauran Garuruwan Iran
  • Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya
  • Leroy Sane ya koma Galatasaray