Aminiya:
2025-05-01@00:31:19 GMT

Ɗan Abacha ya kare mahaifinsa bayan ƙaddamar da littafin IBB

Published: 22nd, February 2025 GMT

Sadiq S. Abacha, ɗan Tsohon Shugaban Mulkin Soji na Najeriya, Janar Sani Abacha, ya bayyana mahaifinsa s matsayin mutum mai nagarta duk da sukar da ake yi masa har yanzu.

A wani rubutu da ya wallafa a shafukan sada zumunta, Sadiq, ya ce an jima ana cin amanar mahaifinsa, amma tarihi zai yanke masa hukunci ta hanyar yin adalci.

Sibil Difens ta cafke mutum 17 kan aikata sata a Yobe Dalilan ƙara kuɗin Jami’ar Gombe — Gwamna Inuwa

“Mutumin nan Abacha—kullum sukarsa da cin amanarsa kuke yi a asirce. Tarihi zai tuna ka a matsayin shugaba nagari, ko da kuwa sun ci gaba da ƙoƙarin rage maka ƙima.

“A matsayina na ɗanka, yau na fi alfahari da kai. Lallai kai ne mutumin da suke so sun zama ko da rabinka ne kuwa,” in ji shi.

Ya kammala rubutunsa da karin maganar Hausawa: “Duk wanda ya yi jifa a kasuwa…”

Rubutun nasa ya zo ne kwanaki kaɗan bayan tsohon shugaban mulkin soja, Ibrahim Badamasi Babangida (IBB), ya ƙaddamar da littafinsa.

Littafin ya jawo cece-kuce sosai, musamman kan soke zaɓen ranar 12 ga watan Yunin 1993.

A cikin littafin, Babangida ya tabbatar da cewar MKO Abiola ne ya lashe zaɓen, amma ya ce wasu a cikin gwamnatinsa, musamman Abacha, suka tilasta masa soke sakamakon zaɓen.

Janar Sani Abacha ya mulki Najeriya daga 1993 zuwa lokacin rasuwarsa a 1998.

Wasu na yaba wa mulkinsa saboda gyaran tattalin arziƙi da tsaro, yayin da wasu ke sukarsa bisa cin hanci da take hakkin ɗan Adam.

A gefe guda kuma, Gumsu Abacha, ɗaya daga cikin ’ya’yan marigayin, ta mayar martani game da littafin da IBB ya ƙaddamar.

A wani saƙo gajere da ta wallafa a shafin X (Twitter), wanda ke kama da habaici.

Haka kuma, ta sake wallafa wasu rubuce-rubuce da ke cewa Babangida ya zargi Abacha da laifuka ne domin ba shi da ikon kare kansa.

Ga hotunan a ƙasa:

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: ya ya Kare Mahaifi

এছাড়াও পড়ুন:

AU ta janye takunkumin da ta ƙaƙaba wa Gabon

Ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU) ta janye takunkuman da ta ƙaƙaba wa Gabon bayan dakatar da ƙasar ta Tsakiyar Afirka saboda juyin mulkin da aka yi a watan Agustan 2023.

Wani taro da aka yi na Kwamitin Zaman Lafiya da Tsaro kan sauyin siyasa a Gabon “ya yi nazari kan ayyukan tare da gano cewa sun yi nasara,” in ji shashen Siyasa da Zaman Lafiya da Tsaro na AU a shafin X a ranar Laraba.

Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya Dalilin da manyan ’yan siyasa ke barin NNPP — APC

Sanarwar ta ce za a yi maraba da Gabon “ta dawo nan da nan, ta ci gaba da shiga ayyuka” a sakatariyar Tarayyar Afirka.

An dakatar da Gabon a lokacin da Janaral Brice Oligui Nguema ya ƙwace mulki bayan kifar da gwamnatin Shugaba Ali Bongo, wanda iyalinsa suka yi mulki tsawon shekaru 55.

Nguema ya yi alkawarin miƙa mulkin ƙasar mai arzikin man fetur ga farar hula bayan shekaru biyu na riƙon ƙwarya, kuma an zaɓe shi a matsayin shugaban farar hula da kashi 94 na kuri’un da aka kaɗa.

Sabon kundin tsarin mulkin da aka samar ya tanadi cewa shugaban ƙasar zai yi mulkin ƙasar da faffaɗan iko.

Matakin da Tarayyar Afirka ta ɗauka ya biyo bayan taron da aka yi a makon da ya gabata tsakanin Nguema da shugaban Ivory Coast Alassane Ouattara, inda Nguema ya nemi goyon baya ta hanyar janye masa takunkuman.

Kasar mai yawan mutane miliyan 2.3 tana fama da rashin ayyukan yi, da katsewar lantarki da rashin ruwan sha, da basussuka a suka yi wa gwamnati katutu duk da arzikin mai da take da shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati Ta ƙaddamar Da Sabon Shafin Intanet Don Inganta Sayayya A Tsakanin Ma’aikatunta 
  • AU ta janye takunkumin da ta ƙaƙaba wa Gabon
  • Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja
  • Rawar da Arewa za ta taka a Zaɓen 2027
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna
  • Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara 
  • Kungiyar Amnesty International Ta Kafa Hujja Kan Ta’asar’Yan Sahayoniyya A Gaza
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Boko Haram Sun Hallaka ‘Yan Zaman Makoki 7, Sun Jikkata Wasu A Borno
  • Har Yanzun Ana Zaman Dar-Dar A Burkina Faso Bayan Kokarin Juyin Mulkin Da Bai SamiNasara Ba