Aminiya:
2025-08-01@20:16:40 GMT

Haɗarin mota ya laƙume rayuka 12 a Neja

Published: 22nd, February 2025 GMT

Aƙalla mutum 12 — ciki har da mata huɗu da maza takwas — sun riga mu gidan gaskiya a sanadiyyar wani mummunan haɗarin mota da ya auku a kan hanyar Lapai zuwa Agaie da ke Jihar Neja.

Wani da lamarin na safiyar wannan Asabar ɗin ya faru a kan idonsa, ya shaida wa Aminiya cewa uku daga cikin matan da suka rasu ’yan gida ɗaya ne.

Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kano ta raba kayan tallafi Ɗan Abacha ya kare mahaifinsa bayan ƙaddamar da littafin IBB

Sai dai wasu fasinjoji uku da suka haɗa da mata biyu da direban motar sun tsallake rijiya da baya, inda a yanzu suke samun kulawa a Babban Asibitin Lapai.

Bayanai sun ce haɗarin ya auku ne bayan wata taho-mu-gama da aka yi tsakanin wata mota ƙirar bas ɗauke da fasinjoji 15 da kuma wata tirela a daidai ƙauyen Nami.

Da yake zantawa da Aminiya ta wayar tarho, direban motar, Mohammed Baba, ya ce lamarin ya auku ne a yayin da suke kan hanyar tafiya Ƙaramar Hukumar Katcha bayan sun taso daga tashar mota ta Kasuwar Gwari da ke birnin Minna.

Direban ya alaƙanta haɗarin da tsautsayi wanda ya ce ya auku ne yayin da direban tirelan ya yi yunƙurin ƙetare wata mota da ke gabansa, lamarin da ya janyo motocin suka yi karo da juna.

Sai dai ya ce tuni direban tirelan ya arce da bayan faruwar lamarin.

Kwamandan Hukumar Kiyaye Haɗura ta Ƙasa FRSC shiyyar Neja, Kumar Tsukwam, ya tabbatar da faruwar lamarin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Haɗarin mota Jihar Neja

এছাড়াও পড়ুন:

’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina

An ceto dukkanin mutane 14 ba tare da wani ya ji rauni ba, amma abin baƙin ciki, wani matashi ɗan shekara 27 mai suna Abba daga garin Funtua ya rasa ransa kafin isowar ’yansanda.

A wani lamari da ya faru a ranar 28 ga watan Yuli da misalin ƙarfe 11:27 na dare, an sake kiran ’yansanda daga ƙauyen Zagaizagi, inda aka sanar da su cewa wasu ’yan bindiga sum hari tare da sace wasu mutane ƙauyen.

’Yansanda sun isa wajen suka gwabza da ’yan bindigar, kuma sun samu nasarar ceto wasu mutane 14 da kuma ƙwato shanun da aka sace guda biyu.

Amma, mutane biyu daga cikin mazauna ƙauyen sun rasa rayukansu a harin.

Rundunar ta ce har yanzu tana ci gaba da ƙoƙarin kamo ’yan bindigar da suka tsere.

Kwamishinan ’yansandan, CP Bello Shehu, ya yaba wa jami’ansa bisa jarumtaka da suka nuna.

Ya kuma buƙaci jama’a da su ci gaba da bai wa ’yansanda sahihan bayanai a kan lokaci.

Ya tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin al’umma a faɗin jihar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Haɗarin tirela ya yi sanadin asarar awaki sama da 100 a Zariya
  • Iran Ta Ce Batun Neman Dakatar Da Tace Uranium Zai Rusa Duk Wata Jarjejeniya Da Ake Son Cimmawa
  • Martani: Har yanzu muna ci gaba da yajin aiki — Ma’aikatan jinya  
  • Mun ci ribar Naira biliyan 414 a cikin wata 6 a Najeriya – Kamfanin MTN
  • Mutane 44 Suka Mutu Bayan Mamakon Ruwa Da Aka Tafka A Beijing
  • Dalilan Da Suka Sa Canada Ta Goyi Bayan Kafa Kasar Falasɗinu
  • Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja
  • Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang