Sibil Difens ta cafke mutum 17 kan aikata sata a Yobe
Published: 22nd, February 2025 GMT
Hukumar Tsaron Farin Kaya ta Sibil Difens (NSCDC), a Jihar Yobe, ta kama wasu mutum 17 da ake zargi da satar kayayyakin lantarki, na’urorin sadarwa a jihar.
Kwamandan rundunar, AS Dandaura, ya tabbatar da kamen a Damaturu, Babban Birnin jihar, inda ya ce an gano wuraren ajiya uku da ake amfani da su don ɓoye kayan sata.
Ya bayyana cewa samamen da aka kai ya taimaka wajen gano wuraren ajiya guda uku—ɗaya a kusa da ofishin Hukumar Alhazai a Damaturu, na biyu a Duriya bayan sabuwar kasuwa, sai kuma na uku a Abbari bypass.
Dandaura ya ce an kama shugaban wata ƙungiyar dillalan kayayyakin bola a yankin, Aliyu Ajakuta, wanda ake zargi da jagorantar aikata satar.
Haka kuma, an cafke wasu da ake zargi da hannu a laifin, ciki har da Umar Sai’adu mai shekara 17, Mohammed Salisu mai shekara 25.
Sauran sun haɗa da Ali Adam mai shekara 18, Ibrahim Mohammed mai shekara 19, Mohammed Musa mai shekara 20, Abdulhamid Mohammed mai shekara 15 da Hassan Dauda mai shekara 18.
Sauran da aka kama sun haɗa da Alhassan Yakubu mai shekara 26, Mohammed Babagana mai shekara 29, Mohammed Bashiru mai shekara 18, Mohammed Bello mai shekara 17, Adamu Abdullahi Usman mai shekara 20, Mustapha Babagana mai shekara 23, Tijani Bako mai shekara 19, Bashiru Adam mai shekara 18 da Lawal Salisu mai shekara 19.
Hukumar ta bayyana cewa ta ƙwato kayayyaki masu yawa daga hannunsu, ciki har da na’urorin sadarwa, igiyoyi masu sulke, manyan karafunan titin, farantin sola, batura, da sauran kayayyaki.
Kwamandan ya jaddada cewa za a gurfanar da waɗanda ake zargi a gaban kotu bayan kammala bincike.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: zargi mai shekara 18 da ake zargi
এছাড়াও পড়ুন:
An shawarci Manoman Kwara Da Su Yi Taka-Tsan-Tsan Saboda Hasashen Ruwa Da Tsawa A Jihar
An yi kira ga manoma a jihar Kwara da su yi taka tsan-tsan domin hasashen za a samu ruwan sama da kuma tsawa da ake hasashen nan da kwanaki masu zuwa.
A wata sanarwa da kwamishinan noma da raya karkara na jihar, Dr, Afees Abolore ya fitar, ya ce a cewar hukumar kula da yanayi ta Najeriya, NiMet, ana sa ran wasu sassa na jihar za su fuskanci ruwan sama da kuma yiwuwar tsawa.
Ya ce za a fuskanci ruwan sama ne da rana da yamma, tsakanin Litinin 28 ga Yuli da Laraba 30 ga Yuli, 2025.
Ya yi bayanin cewa duk da cewa ba a sami ruwan sama ba tukuna, yanayin da ke gaba zai iya kawo cikas ga ayyukan noma da ake ci gaba da yi, musamman ga masu sharefilaye, da watsin taki, ko girbin amfanin gona.
Ya yi nuni da cewa wuraren da ke da ƙarancin magudanar ruwa ko kuma waɗanda ke kusa da hanyoyin ruwa na iya zama mafi haɗari ga ambaliya.
Sanarwar ta shawarci manoman da su daina amfani da takin zamani domin gujewa wankewa da almubazzaranci, da kuma girbi manyan amfanin gona da wuri domin hana lalacewa daga ruwan sama.
Yana ƙarfafa manoma da su ɗauki hasashen da gaske kuma su hanzarta yin aiki don rage cikas da kiyaye rayuwarsu.
REL/ALI MUHAMMAD RABIU