Sibil Difens ta cafke mutum 17 kan aikata sata a Yobe
Published: 22nd, February 2025 GMT
Hukumar Tsaron Farin Kaya ta Sibil Difens (NSCDC), a Jihar Yobe, ta kama wasu mutum 17 da ake zargi da satar kayayyakin lantarki, na’urorin sadarwa a jihar.
Kwamandan rundunar, AS Dandaura, ya tabbatar da kamen a Damaturu, Babban Birnin jihar, inda ya ce an gano wuraren ajiya uku da ake amfani da su don ɓoye kayan sata.
Ya bayyana cewa samamen da aka kai ya taimaka wajen gano wuraren ajiya guda uku—ɗaya a kusa da ofishin Hukumar Alhazai a Damaturu, na biyu a Duriya bayan sabuwar kasuwa, sai kuma na uku a Abbari bypass.
Dandaura ya ce an kama shugaban wata ƙungiyar dillalan kayayyakin bola a yankin, Aliyu Ajakuta, wanda ake zargi da jagorantar aikata satar.
Haka kuma, an cafke wasu da ake zargi da hannu a laifin, ciki har da Umar Sai’adu mai shekara 17, Mohammed Salisu mai shekara 25.
Sauran sun haɗa da Ali Adam mai shekara 18, Ibrahim Mohammed mai shekara 19, Mohammed Musa mai shekara 20, Abdulhamid Mohammed mai shekara 15 da Hassan Dauda mai shekara 18.
Sauran da aka kama sun haɗa da Alhassan Yakubu mai shekara 26, Mohammed Babagana mai shekara 29, Mohammed Bashiru mai shekara 18, Mohammed Bello mai shekara 17, Adamu Abdullahi Usman mai shekara 20, Mustapha Babagana mai shekara 23, Tijani Bako mai shekara 19, Bashiru Adam mai shekara 18 da Lawal Salisu mai shekara 19.
Hukumar ta bayyana cewa ta ƙwato kayayyaki masu yawa daga hannunsu, ciki har da na’urorin sadarwa, igiyoyi masu sulke, manyan karafunan titin, farantin sola, batura, da sauran kayayyaki.
Kwamandan ya jaddada cewa za a gurfanar da waɗanda ake zargi a gaban kotu bayan kammala bincike.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: zargi mai shekara 18 da ake zargi
এছাড়াও পড়ুন:
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
“Haka kuma an kama wata mata mai shekaru 34 da ake zargi da hannu a lamarin, tare da wasu masu gidan marayu guda biyu da ke Abuja da Jihar Nasarawa, inda aka gano wasu yaran da ake kyautata zaton an yi safarar su. Wasu daga cikin gidajen marayun da aka gano ana amfani da su ne a matsayin cibiyoyin ajiye yara, inda ake jiran ‘kwace’ ko sayar da su da sunan daukar nauyin marayu.”
Ya ce, “An gano gidajen marayu guda hudu da ke Kaigini, Kubwa Edpressway Abuja; Masaka Area 1, Mararaba kusa da Abaca Road; da kuma Mararaba bayan Kasuwar Duniya suna da alaka da wannan kungiya, kuma ana ci gaba da bincike a kansu.”
Ya kara da cewa, daya daga cikin masu korafin ya bayyana cewa ya biya Naira miliyan 2.8 a matsayin kudin daukar yaro, sannan ya biya Naira 100,000 a matsayin kudin shawara ga daya daga cikin ‘yan kungiyar.
Sanarwar ta kara da cewa, “Wani mai korafi ya ce shi ma ya biya Naira miliyan 2.8 kudin daukar yaro da Naira 100,000 kudin shawara ga wani dan kungiyar.
“An canza sunayen yawancin yaran da aka ceto, lamarin da ya kara wahalar da bincike da gano asalinsu,” in ji sanarwar.
Darakta Janar ta NAPTIP, Binta Adamu Bello, ta bayyana damuwarta kan wannan lamari, inda ta ce safarar yara ta zama babbar matsala a kasa.
Ta hanyar Adekoye, DG din ta nuna damuwa game da yadda wasu gidajen marayu ke amfani da raunin jama’a wajen aiwatar da safarar yara.
Ta ce, “Abin takaici ne yadda wasu masu mugunta da ke da sunayen kwararru da matsayi a cikin al’umma, suke amfani da matsayin su wajen yaudarar mutanen da ke cikin mawuyacin hali, su yi safarar ‘ya’yansu, da dama daga cikinsu ma sun tsira ne daga halaka a lokacin rikice-rikicen al’umma ko na manoma da makiyaya, sannan a sayar da su ga iyaye masu neman haihuwa a matsayin daukar yaro ba tare da sahihin izinin iyayensu ba.
“Wannan abin ba za a yarda da shi ba, kuma wadanda aka kama kan wannan mugun aiki za su fuskanci hukuncin doka yadda ya kamata.
“’Ya’yanmu ba kayayyaki ba ne da za a ajiye su a gidajen marayu a sayar ga mai biyan mafi tsada. Wannan dole ya tsaya,” in ji ta.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA