Aminiya:
2025-08-01@06:57:35 GMT

Gwamnatin Najeriya za ta sake ƙara kuɗin lantarki

Published: 3rd, February 2025 GMT

Gwamnatin Tarayya ta sanar das shirye-shiryenta na sake kara kudin wutar lantarki nan da watanni masu zuwa.

Ta bayyana cewa ana tsara karin ta yadda zai zo da tallafi ga masu karamin karfi cikin masu amfani da wutar.

Mashawarciyar Shugaban Kasa kan Makamashi, Olu Verheijen, ce ta sanar da hakan a Babban Taron Shugabannin Lantarki na Kasashen Afirka da ke gudana a Dar es Salaam, hedikwatar kasar Tanzania.

A yayin taron ta gabatar wa mahalarta da shirin na Najeriya na kashe Dala biliyan 32 domin inganta wutar lantarki zuwa shekarar 2030.

Batun karin na zuwa ne bayan a bara gwamnatin ta yi ninka kudin wuta sau uku ga kwastomomi da ke amfani da Band A.

A yanzu kuma kamfanonin rarraba wutar lantarki, wadanda basuka suka riga suka yi musu katutu, sun matsa wa gwamnatin lamba ta bari su kara kudi domin samar da wutar yadda za su share hawayen kwastomominsu.

A watan Afrilun 2024 Hukumar Wutar Lantarki ta Kasa (NERC) ta yi karin kudin wuta da kashi 300%, daga N68 zuwa N225 a kan kowane kilowat ga masu amfani da Band A.

Da yake sanar karin, Mataimakin Shugaban NERC, Musliu Oseni, ya ce kashi 15% na masu amfani da wutar ne ya shafa, kuma zai inganta samuwar wutar.

Hakazalika Ministan Lantarki, Adebayo Adelabu, ya bayyana cewa idan aka ci gaba da biyan tallafi ga masu amfani da Band A, yawan kudin da gwamnati ke biya na tallafin a shekara zai karu zuwa Naira tiriliyan biyu.

Amma dai daga bisani an rage kudin zuaw N209.5.

Sabon kafin farashi

Game da sabon karin kudin, hadimar shugaban kasan ta bayyana cewa Najeriya na kokarin samar da tsarin samun wutar lantarki gwargwadon yadda aka biya kudin, domin jawo masu zuwa jari a bangaren.

Ta shaida wa taron cewa, “Daya daga cikin kalubalen da muke  kokari magancewa nan da ’yan watanni masu zuwa shi ne komawa tsarin shan wutar lantarki gwargwadon yadda aika biya.

“Da haka ne bangaren zai tara kudaden da ake bukata domin jawo ’yan kasuwa masu zuwa jari tare da kare talakawa da masu rauni daga cuta.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gwamnati Karin kudin wuta Lantarki wutar lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya karɓi baƙuncin ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar ƙananan hukumomin Kiru da Bebeji na Jihar Kano, Abdulmumin Jibrin Kofa.

Aminiya ta ruwaito cewa Kofa, wanda makusanci ne ga jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, kuma ɗaya daga cikin jiga-jigai a jam’iyyar NNPP, ya ziyarci shugaban ƙasar ne a yau Laraba.

Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya Tattalin arzikin Nijeriya zai ci gaba da bunƙasa har zuwa baɗi — IMF

Har yanzu dai babu wasu bayanai dangane da abin da suka tattauna, amma ziyarar wadda hadimai daga ɓangarorin biyu suka riƙa yaɗawa na ci gaba da ɗaukar hankalin jama’a.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAJERIYA A YAU: Me dokar kasa ta ce kan karin wa’adin aiki da Shugaban Kasa ke yi?
  • INEC Ta Gudanar da Taron Masu Ruwa da Tsaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi na Babura/Garki
  • NNPCL ya sake haƙa sabbin rijiyoyin man fetur 4 a Kolmani
  • Kamfanin NNPCL ya sake haka sabbin rijiyoyin man fetur 4 a Kolmani
  • Samar da makamashi mai tsafta na zamani shi ne fatanmu — Guterres
  • Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • An Kaddamar da Makon MNCH na 2025, Ya Rarraba Fakitin Bayarwa 6,000, Kayan C/S 500
  • Gwamnatin Sakkwato Ta Sayo Manyan Tan-tan 250 Na Sama Da Naira Biliyan 22
  • Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana