Aminiya:
2025-06-15@13:45:26 GMT

Gwamnatin Najeriya za ta sake ƙara kuɗin lantarki

Published: 3rd, February 2025 GMT

Gwamnatin Tarayya ta sanar das shirye-shiryenta na sake kara kudin wutar lantarki nan da watanni masu zuwa.

Ta bayyana cewa ana tsara karin ta yadda zai zo da tallafi ga masu karamin karfi cikin masu amfani da wutar.

Mashawarciyar Shugaban Kasa kan Makamashi, Olu Verheijen, ce ta sanar da hakan a Babban Taron Shugabannin Lantarki na Kasashen Afirka da ke gudana a Dar es Salaam, hedikwatar kasar Tanzania.

A yayin taron ta gabatar wa mahalarta da shirin na Najeriya na kashe Dala biliyan 32 domin inganta wutar lantarki zuwa shekarar 2030.

Batun karin na zuwa ne bayan a bara gwamnatin ta yi ninka kudin wuta sau uku ga kwastomomi da ke amfani da Band A.

A yanzu kuma kamfanonin rarraba wutar lantarki, wadanda basuka suka riga suka yi musu katutu, sun matsa wa gwamnatin lamba ta bari su kara kudi domin samar da wutar yadda za su share hawayen kwastomominsu.

A watan Afrilun 2024 Hukumar Wutar Lantarki ta Kasa (NERC) ta yi karin kudin wuta da kashi 300%, daga N68 zuwa N225 a kan kowane kilowat ga masu amfani da Band A.

Da yake sanar karin, Mataimakin Shugaban NERC, Musliu Oseni, ya ce kashi 15% na masu amfani da wutar ne ya shafa, kuma zai inganta samuwar wutar.

Hakazalika Ministan Lantarki, Adebayo Adelabu, ya bayyana cewa idan aka ci gaba da biyan tallafi ga masu amfani da Band A, yawan kudin da gwamnati ke biya na tallafin a shekara zai karu zuwa Naira tiriliyan biyu.

Amma dai daga bisani an rage kudin zuaw N209.5.

Sabon kafin farashi

Game da sabon karin kudin, hadimar shugaban kasan ta bayyana cewa Najeriya na kokarin samar da tsarin samun wutar lantarki gwargwadon yadda aka biya kudin, domin jawo masu zuwa jari a bangaren.

Ta shaida wa taron cewa, “Daya daga cikin kalubalen da muke  kokari magancewa nan da ’yan watanni masu zuwa shi ne komawa tsarin shan wutar lantarki gwargwadon yadda aika biya.

“Da haka ne bangaren zai tara kudaden da ake bukata domin jawo ’yan kasuwa masu zuwa jari tare da kare talakawa da masu rauni daga cuta.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gwamnati Karin kudin wuta Lantarki wutar lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin Tarayya ta roƙi ƙasashen Isra’ila da Iran da su daina rikici, su zauna lafiya su sasanta tsakaninsu. 

A wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Waje ta fitar, ta bayyana damuwa kan yadda rikicin ke ƙara ta’azzara, inda ta nemi ɓangarorin biyu da su kai zuciya nesa don samar da zaman lafiya a duniya baki ɗaya.

Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — Dalung

Sanarwar ta ce faɗa da ramuwar gayya na jefa rayukan fararen hula cikin hatsari, kuma yana iya haddasa rikici mai muni a yankin Gabas ta Tsakiya, wanda hakan zai iya barazana ga tsaron duniya da kuma ci gaban tattalin arziƙi dunuya.

“Mu a matsayimmu na ƙasa mai son zaman lafiya, muna roƙon ƙasashen da ke rikici da su zauna su tattauna maimakon su ci gaba da faɗa.”

Gwamnatin Tarayya ta kuma yi kira ga ƙasashen duniya, musamman Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya, da su ɗauki matakai don hana yaɗuwar rikicin da kuma samo hanyar warware matsalar.

Sanarwar ta ƙara da cewa amfani da ƙarfin soji ba shi da amfani matuƙa, domin faɗa ba zai kawo sauƙi ba.

Najeriya ta ce a shirye ta ke ta bayar da taimako domin hana yaɗuwar rikicin da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran ta sake kai hare-haren martani kan Isra’ila
  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Isra’ila da Iran su daidaita rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu
  • An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia
  • Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa
  • Gwamnatin Bauchi Ta Fara Shirin Kirkirar Sabbin Masarautu Da Sarakuna Da Gundumomi