Matakin Sanya Karin Harajin Kwastam Ba Zai Daidaita Matsalar Da Amurka Ke Fuskantar Ba
Published: 3rd, February 2025 GMT
A kwanan nan, kasar Amurka ta sanar da sanya karin harajin kwastam da ya kai kaso 10% kan kayayyakin da kasar Sin ke fitar da su zuwa kasuwannin Amurka. Wannan mataki ya keta ka’idojin kungiyar cinikayya ta duniya WTO, wanda kuma zai lalata huldar dake tsakanin Sin da Amurka a fannin cinikayya. Yanzu haka, kasar Sin ta ce za ta kai kara ga kungiyar WTO, gami da daukar matakan da suka wajaba wajen kare moriyarta.
A ganin kwararru masu nazarin al’amuran duniya, dalilin da ya sa sabuwar gwamnatin kasar Amurka daukar matakin nan na sanya karin haraji shi ne domin neman tilastawa sauran kasashe su biya kudi, ta yadda kasar Amurka za ta samu damar sassanta matsalar tattalin arziki da take fuskanta. Sai dai an ce matakin zai sa jama’ar kasar Amurka kashe karin kudi wajen sayen kayayyakin masarufi, da rasa dimbin guraben aikin yi.
A nata bangare, matakin da Amurka ta dauka zai sa yawan harajin kwastam da ake kakabawa kayayyakin da kasar Sin ke fitar da su zuwa Amurka kaiwa kimanin kaso 30. Amma hakan ba zai yi tasiri sosai kan tattalin arzikin kasar Sin ba, saboda tun tuni kasar ta fara daidaita manufar fitar da kayayyakinta. Yanzu haka, yawan kayayyakin da Sin take fitarwa zuwa Amurka ya riga ya ragu zuwa kasa da kaso 15%, cikin dukkan kayayyakin da Sin ke fitar da su kasuwannin ketare.
Ban da haka, matakin da kasar Amurka ta dauka na sanya karin harajin kwastam bai shafi Sin kawai ba, wanda shi ma ya jibanci kasashen Mexico da Canada, wadanda suka tabbatar da cewa za su sanya karin haraji kan kayayyakin kasar Amurka don mayar da martani ga matakin Amurka. (Bello Wang)
কীওয়ার্ড: kasar Amurka sanya karin
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya ce Sin na kira ga Amurka, da ta gaggauta dakatar da shuka kiyayya, da haifar da tashin hankali, da rura wutar gaba a tekun kudancin kasar Sin, kana ta kyale a dawo da yanayin zaman lafiya da daidaito a yankin. Lin Jian, ya bayyana hakan ne yau Litinin, yayin taron manema labarai da aka saba gudanarwa, lokacin da aka yi masa tambaya kan batun.
Wasu rahotanni daga kafofin watsa labarai sun bayyana cewa, a baya bayan nan, sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio, ya fitar da sanarwa dake cewa Amurka na goyon bayan kasar Philippines, game da watsi da ta yi da tsare-tsaren kasar Sin na kafa yankin kare muhallin halittu a tsibirin Huangyan Dao.
Lin ya ce “Mun gabatar da kakkarfan korafi a yau, dangane da kuskuren da Amurka ta tafka. Tsibirin Huangyan Dao yankin kasar Sin ne tun fil azal”, kuma kafa yankin kare muhallin halittu a tsibirin na karkashin ikon mulkin kai na Sin, wanda hakan ke nufin yana bisa turba, ya dace da doka, bai kuma cancanci suka ba. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp