HausaTv:
2025-05-01@06:16:07 GMT

 An Fito Da Gawawwakin Shahidai Fiye Da 400 Daga Karkashin Baraguzai A Gaza

Published: 3rd, February 2025 GMT

Ma’aikatan Agaji suna ci gaba da fito da gawawwakin shahidan Falasdinawa da Isra’ila ta rushe gidaje akansu, a tsawon lokacin yaki,wasu kuma akan hanyoyi.

Wani jami’in agaji ya ce, bayan gushewar fiye da shekara daya na yaki, da wuya suke iya samun cikakkiyar gawar wani daga cikin shahidai, sai dai  rabi da rabi, a wasu wuraren ma dai sai dai kasusuwa.

Ya zuwa yanzu dai an sami gawawwakin da sun kai 458 kamar kakakin ma’aikatar kiwon lafiya ta Falasdinu Dr.  Khalil Dakran ya ambata.

Ma’aikatar kiwon lafiyar ta Falasdinawa tana kirdadon cewa za a iya samun gawawwakin da suke tsakanin 4000, zuwa 5000 a karkashin baraguzai a fadin Falasdinu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

 Bom Da Ya Tashi A Arewa Maso Gabashin Najeriya Ya Kashe Mutane 6

Wani bon kirar hannu da aka dasa akan hanyar dake hada Rann da Gamboru a jihar Borno ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 6.

Daga cikin wadanda su ka rasa rayukansu sanadiyyar tashin bom din sun hada mata da kananan yara kamar yadda majiyar ‘yan sanda ta sanar.

Kungiyar nan mai suna; gwamnatin musulunci a yammacin Afirka ce ta sanar da daukar alhakin kai hari na ranar Litinin din da ta gabata.

Bugu da kari sauran wadanda su ka rasa rayukan nasu manoma ne da suke cikin motar a-kori-kura da ta taka nakiya.

Baya ga wadanda su ka rasa rayukansu, wasu mutanen su 3 sun jikkata,kuma tuni an dauke su zuwa asibiti domin yi musu magani.

Wani dan sintiri da yake aiki da rundunar fararen hula masu taimakawa jami’an tsaro, Abba Madu, ya shaida wa manema labaru cewa; Da alamu an dasa bom din domin ya tashi da jami’an tsaro da suke yin sintiri akan wannan hanyar.

Kungiyoyin ‘yan ta’adda sun saba dasa irin wadannan nakiyoyin da bama-baman akan hanyar da jami’an tsaro suke bi.

Kungiyar nan da take kiran kanta; Gwamnatin Musulunci a yammacin Afirka wacce a takaice ake kira; “ISWAP” ce ta dauki nauyin kai harin.

Tun a 2009 ne yankin Arewa maso gabashin kasar ta Najeriya yake fama da matsalar kungiyoyi masu dauke da makamai da su ka hada Bokoharam, sannan kuma daga baya waje 2016, kungiyar gwamnatin musulunci a yammacin Afirka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kar A Mika Wuya Ga “Damisar Takarda”
  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • Katafaren Jirgin Daukar Jiragen Yaki Na Kasar Amurka Harry Truman Zai Fice Daga Tekun Maliya
  •  Bom Da Ya Tashi A Arewa Maso Gabashin Najeriya Ya Kashe Mutane 6
  •  Falasdinawa 40 Sun Yi Shahada A Cikin Sa’oi 24 A Gaza
  • Nijeriya Na Ke Yi Wa Biyayya Ba Wani Ko Jam’iyya Ba – El-Rufai
  • HKI Tana Amfani Yunwa A Matsayin Makamin Yaki  A Kan Falasdinawa A Gaza
  • Makafi 37 Sun Zana Jarabawar JAMB A Bauchi
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Jaddada Wajabcin Komawa Kan Shirin Tsagaita Bude Wuta A Gaza
  • Ƴansanda Sun Kama Ƴan Daba 33 A Kano