Jami’an tsaro sun mamaye sakatariyar PDP bayan ɓarkewar rikici
Published: 29th, January 2025 GMT
Jami’an tsaro sun mamaye Sakatariyar Jam’iyyar PDP, bayan rikici ya ɓarke kan shugabancin jam’iyyar.
Rikicin ya kunno kai ne tsakanin Samuel Anyanwu da Sunday Ude-Okoye kan wanda ke da haƙƙin zama Sakataren jam’iyyar na ƙasa.
Matashiyar da ta watsa wa mai naƙuda tafasasshen ruwa ta shiga hannu Me kuka sani game da ficewar Mali, Nijar, da Burkina Faso daga ECOWAS?Rikicin ya fara ne lokacin da duka mutane biyun suka iso taron kwamitin amintattun.
A lokacin taron, wani hadimin Anyanwu ya tilasta wa Ude-Okoye fita daga zauren taron, wanda hakan ya janyo gardama tsakanin magoya bayan ɓangarorin biyu.
Jami’an tsaro sun shiga tsakani domin kwantar da tarzoma.
Matsalar ta samo asali ne bayan Anyanwu ya yi murabus daga kujerarsa don tsayawa takarar Gwamnan Jihar Imo, takarar da bai yi nasara ba.
A lokacin da ba ya nan, ɓangaren jam’iyyar na Kudu maso Gabas ya naɗa Ude-Okoye a matsayin sabon sakataren jam’iyyar.
Amma bayan Anyanwu ya faɗi a zaɓen gwamna, ya yi ƙoƙarin karɓe kujerarsa a jam’iyyar, wanda hakan ya haddasa rikici.
A ranar 20 ga watan Disamban 2024, kotun ɗaukaka ƙara da ke Enugu ta tabbatar da hukuncin wata babbar kotu da ta tuɓe Anyanwu daga kujerar sakataren jam’iyyar, tare da tabbatar da Ude-Okoye a matsayin halastaccen sakatare.
Anyanwu ya ɗaukaka ƙara tare da neman dakatar da hukuncin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Sakatare Sakatariya
এছাড়াও পড়ুন:
Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?
Shugabannin Rundunar tsaro da Tinubu ya sallama sun hada da shugaban rundunar tsaro ta kasa Janar Christopher Musa da shugaban sojojin ruwa, Emmanuel Ikechukwu Ogalla da shugaban sojojin sama Hassan Abubakar.
Wadanda suka maye gurbin su da idanu ya koma kan hobbasar kwazon da za su nuna su ne shugaban rundunar tsaro Olufemi Oluyede, shugaban sojojin kasa Waidi Shaibu, shugaban sojojin ruwa Idi Abbas da shugaban sojojin sama S.K Aneke sai kuma shugaban rundunar leken asiri, EAP Undiendeye wanda ya ci-gaba da rike kujerar sa.
Yan Nijeriya sun jima suna kukan duk da kwarewa da gogewar jami’an sojojin Nijeriya da irin makuddan kudaden da gwamnati ke kashewa a sha’anin tsaro a kowace shekara amma matsalar kullum gaba- gaba take kara yi.
Yankuna da dama a Nijeriya musamman a Arewa- Maso- Yamma, Arewa- Maso- Gabas da Arewa ta tsakiya sun zama lahira kusa a bisa ga yadda barayin daji ke garkuwa da mutane, kone garuruwa da yi wa jama’a kisan kare dangi.
Gagarumar matsalar wadda tuni ta zama tamkar ruwan dare a tsayin shekaru ta ci dimbin rayuka da dukiyoyin al’umma ba adadi ba tare da samun gagarumar nasarar dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a cikin al’umma ba.
Masana tsaro sun bayyana ra’ayoyi mabambanta kan sauye- sauyen. Wasu na ganin cewa sabbin jini za su iya kawo canji, yayin da wasu suka yi gargadin cewa sauya shugabanni kadai ba zai wadatar ba idan ba a yi gyaran tsari ba.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA