Jami’an tsaro sun mamaye sakatariyar PDP bayan ɓarkewar rikici
Published: 29th, January 2025 GMT
Jami’an tsaro sun mamaye Sakatariyar Jam’iyyar PDP, bayan rikici ya ɓarke kan shugabancin jam’iyyar.
Rikicin ya kunno kai ne tsakanin Samuel Anyanwu da Sunday Ude-Okoye kan wanda ke da haƙƙin zama Sakataren jam’iyyar na ƙasa.
Matashiyar da ta watsa wa mai naƙuda tafasasshen ruwa ta shiga hannu Me kuka sani game da ficewar Mali, Nijar, da Burkina Faso daga ECOWAS?Rikicin ya fara ne lokacin da duka mutane biyun suka iso taron kwamitin amintattun.
A lokacin taron, wani hadimin Anyanwu ya tilasta wa Ude-Okoye fita daga zauren taron, wanda hakan ya janyo gardama tsakanin magoya bayan ɓangarorin biyu.
Jami’an tsaro sun shiga tsakani domin kwantar da tarzoma.
Matsalar ta samo asali ne bayan Anyanwu ya yi murabus daga kujerarsa don tsayawa takarar Gwamnan Jihar Imo, takarar da bai yi nasara ba.
A lokacin da ba ya nan, ɓangaren jam’iyyar na Kudu maso Gabas ya naɗa Ude-Okoye a matsayin sabon sakataren jam’iyyar.
Amma bayan Anyanwu ya faɗi a zaɓen gwamna, ya yi ƙoƙarin karɓe kujerarsa a jam’iyyar, wanda hakan ya haddasa rikici.
A ranar 20 ga watan Disamban 2024, kotun ɗaukaka ƙara da ke Enugu ta tabbatar da hukuncin wata babbar kotu da ta tuɓe Anyanwu daga kujerar sakataren jam’iyyar, tare da tabbatar da Ude-Okoye a matsayin halastaccen sakatare.
Anyanwu ya ɗaukaka ƙara tare da neman dakatar da hukuncin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Sakatare Sakatariya
এছাড়াও পড়ুন:
Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu
Gwamnatin Tarayya ta roƙi ƙasashen Isra’ila da Iran da su daina rikici, su zauna lafiya su sasanta tsakaninsu.
A wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Waje ta fitar, ta bayyana damuwa kan yadda rikicin ke ƙara ta’azzara, inda ta nemi ɓangarorin biyu da su kai zuciya nesa don samar da zaman lafiya a duniya baki ɗaya.
Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — DalungSanarwar ta ce faɗa da ramuwar gayya na jefa rayukan fararen hula cikin hatsari, kuma yana iya haddasa rikici mai muni a yankin Gabas ta Tsakiya, wanda hakan zai iya barazana ga tsaron duniya da kuma ci gaban tattalin arziƙi dunuya.
“Mu a matsayimmu na ƙasa mai son zaman lafiya, muna roƙon ƙasashen da ke rikici da su zauna su tattauna maimakon su ci gaba da faɗa.”
Gwamnatin Tarayya ta kuma yi kira ga ƙasashen duniya, musamman Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya, da su ɗauki matakai don hana yaɗuwar rikicin da kuma samo hanyar warware matsalar.
Sanarwar ta ƙara da cewa amfani da ƙarfin soji ba shi da amfani matuƙa, domin faɗa ba zai kawo sauƙi ba.
Najeriya ta ce a shirye ta ke ta bayar da taimako domin hana yaɗuwar rikicin da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankin.