Kwalejin Sadarwa ta Jami’ar Bayero Kano (BUK) ta hada kai da kungiyar ‘yan jarida ta Najeriya SNB domin gudanar da wani taron tattaunawa kan kalubalen aikin jarida na bincike da bayanai a yankin Arewa maso yammacin Najeriya.

 

Taron wanda ya gudana a BUK, ya tattaro ‘yan jarida, malamai, da kwararru kan harkokin yada labarai, inda suka tattauna kan yanayin aikin jarida na bincike a yankin.

 

Taron dai na da nufin gano kalubalen da ‘yan jarida ke fuskanta da kuma lalubo hanyoyin bunkasa aikin jarida na bincike a yankin Arewa maso yammacin Najeriya.

 

A jawabin sa na farko, shugaban SNB wanda kuma shine Shugaban jami’ar tarayya Kashere Gombe Farfesa Umaru Pate ya jaddada muhimmancin bayar da bayanai ta hanyar magance matsalar cin hanci da rashawa, shugabanci, da kalubalen ci gaba a yankin Arewa maso Yamma.

 

Tsohon mai watsa labarai Ado Warawa ya bayyana abubuwan da ya gani a aikin jarida na bincike, yayin da Farfesa Sulaiman Yar’adua na sashen sadarwa na BUK ya tattauna kan kalubalen da ke damun aikin jarida na bincike a yankin.

 

Yar’adua ya yi kira da a kara saka hannun jari wajen horar da ‘yan jarida da kuma tsauraran tsarin shari’a don kare masu aikin yada labarai.

 

Zauren ya ba da dama ga mahalarta don musanyar fahimta da shawarwari.

 

Sashen Sadarwa da Kungiyar Masu Watsa Labarai ta Najeriya sun yi alkawarin ci gaba da shirya irin wadannan tarukan don karfafa ayyukan yada labarai da kuma samar da rahotanni masu tasiri a Najeriya.

 

KHADIJAH ALIYU/Wababe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jarida Taro aikin jarida na bincike

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.

Daga Abdullahi Shettima

Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Uba Sani, ya wakilci Nijeriya a taron ƙoli na biranen Asiya da ya gudana a ƙasar Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE), inda ya gabatar da kudirorin sauyin ci gaban Kaduna.

Taron ya samu halartar manyan baki daga ƙasashe sama da 150, ciki har da gwamnoni, shugabannin birane da jagororin kasuwanci daga Asiya, Fasifik, Turai da Afirka. Taken taron shi ne “Haɗin Gwiwa. Ƙarfafawa. Sauyi.”

A jawabinsa mai taken “Gina Haɗin Gwiwa Domin Ci Gaban Kowa,” Gwamna Uba Sani ya bayyana yadda Kaduna ke samun nasara a fannoni da dama kamar gyaran birane, bunƙasa noma da tallafawa jama’a. Ya ce tsarin ci gaban jihar yana dogara ne kan faɗaɗa damar tattalin arziki, kare marasa ƙarfi, da ƙarfafa jama’a su cim ma nasara a rayuwarsu.

Haka kuma, ya halarci baje kolin birnin Dubai mai taken “Sauya Arewa a Nijeriya: Jagoranci, Ƙirƙira da Tasirin Zamantakewa,” inda ya jaddada muhimmancin jagoranci mai nagarta da amfani da fasaha wajen buɗe damarmaki ga al’umma.

A yayin taron, Gwamnan ya gudanar da ganawa ta musamman da Marwan Bin Galita, Darakta-Janar na birnin Dubai, inda suka tattauna batutuwan kirkirar makamashin sharar gida, kula da sharar zamani, da tsare-tsaren gine-ginen birane na zamani.

Duk ɓangarorin biyu sun amince da zurfafa haɗin kai a fannin fasaha da musayar ƙwarewa domin tallafawa sauyin tattalin arzikin Kaduna zuwa mai ɗorewa.

Gwamna Sani ya bayyana cewa halartar Kaduna a taron (APCS 2025) na nuna shirin jihar na shiga sahun gaba wajen yin haɗin kai, ƙirƙira da zama abin koyi a fannin ci gaba mai ɗorewa — a Najeriya da duniya baki ɗaya.

Karshe.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya yanke hulɗa da Amurka kawai — Sheikh Gumi
  • Larijani: Iran Ba Ta Tsoron Gudanar Da Tattaunawa, Amma Ta Zama Mai Amfani
  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya
  • Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa
  • Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi