Kwalejin Sadarwa ta Jami’ar Bayero Kano (BUK) ta hada kai da kungiyar ‘yan jarida ta Najeriya SNB domin gudanar da wani taron tattaunawa kan kalubalen aikin jarida na bincike da bayanai a yankin Arewa maso yammacin Najeriya.

 

Taron wanda ya gudana a BUK, ya tattaro ‘yan jarida, malamai, da kwararru kan harkokin yada labarai, inda suka tattauna kan yanayin aikin jarida na bincike a yankin.

 

Taron dai na da nufin gano kalubalen da ‘yan jarida ke fuskanta da kuma lalubo hanyoyin bunkasa aikin jarida na bincike a yankin Arewa maso yammacin Najeriya.

 

A jawabin sa na farko, shugaban SNB wanda kuma shine Shugaban jami’ar tarayya Kashere Gombe Farfesa Umaru Pate ya jaddada muhimmancin bayar da bayanai ta hanyar magance matsalar cin hanci da rashawa, shugabanci, da kalubalen ci gaba a yankin Arewa maso Yamma.

 

Tsohon mai watsa labarai Ado Warawa ya bayyana abubuwan da ya gani a aikin jarida na bincike, yayin da Farfesa Sulaiman Yar’adua na sashen sadarwa na BUK ya tattauna kan kalubalen da ke damun aikin jarida na bincike a yankin.

 

Yar’adua ya yi kira da a kara saka hannun jari wajen horar da ‘yan jarida da kuma tsauraran tsarin shari’a don kare masu aikin yada labarai.

 

Zauren ya ba da dama ga mahalarta don musanyar fahimta da shawarwari.

 

Sashen Sadarwa da Kungiyar Masu Watsa Labarai ta Najeriya sun yi alkawarin ci gaba da shirya irin wadannan tarukan don karfafa ayyukan yada labarai da kuma samar da rahotanni masu tasiri a Najeriya.

 

KHADIJAH ALIYU/Wababe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jarida Taro aikin jarida na bincike

এছাড়াও পড়ুন:

Hajj 2025: Kaduna Ta Gaddamar Da Ayarin Likitoci Da Za Su Kula Da Alhazan Jihar

Gwamna Uba Sani na Jihar Kaduna ya kaddamar da ayarin likitoci su tara domin kula da lafiyar maniyata aikin hajjin na wannan shekaran.

Shugaban Hukumar Jin Daɗin Alhazan Jihar Kaduna, Malam Salihu S. Abubakar, ne ya bayyana hakan bayan ganawar farko da ayarin da kuma shugabannin hukumar.

Ayarin likitocin ƙarƙashin jagorancin Dr. Bello Jamoh, za su gudanar da cikakken binciken lafiyar maniyata kafin tafiyar su zuwa kasa mai tsarki da zai gudana a sansanin alhazai da ke Mando, Kaduna.

Sannan kuma za su bayar da taimakon gaggawa a kasar Saudiyya tare da haɗin gwiwar Ayarin likitocin daga Hukumar Hajji ta Kasa (NAHCON).

Shugaban hukumar ya ce mambobin ayarin za su kasance cikin tsari na duba lafiyar mahajjata a tsawon lokacin aikin hajjin.

“Lafiya maniyata aikin hajjin tana da matuƙar muhimmanci, mun zaɓi ayarin ne bisa ƙwarewarsu, kuma muna da tabbacin za su bayar da ingantaccen kulawa ta lafiya a lokacin aikin hajjin,” In ji shi.

Shugaban ya ƙara da cewa za a gudanar da cikakken gwajin lafiya ga dukkan masu niyyar zuwa aikin Hajj, musamman don gano mata masu juna biyu.

Babu sassauci ko kaɗan wajen barin mata masu juna biyu su tafi Hajj.” in ji Malam Salihu, yana mai jaddada cewa gudunmuwar da ayarin likitocin za su bada wajen tabbatar da wannan doka, na da muhimmanci don bin ƙa’idodin aikin Hajjin.

Ya ja hankalin ayarin likitocin su gudanar da aikinsu cikin ƙwarewa da sadaukarwa, domin tabbatar da cewa mahajjata sun samu aikin hajji mai sauƙi cikin koshin lafiya.

 

Adamu Yusuf

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hajj 2025: Kaduna Ta Gaddamar Da Ayarin Likitoci Da Za Su Kula Da Alhazan Jihar
  • Za A Yi Allurar Rigakafi Ga Dabbobi Sama Da Miliyan Daya A Babura
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Shirya Fara Tantance ‘Yan Fansho
  • Sabbin Bayanai Kan Fashe-Fashe Wasu Abubuwa A Tashar Jiragen Ruwan Kasar Iran
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Quneitra Na Kasar Siriya Tare Da Kafa Shingen Bincike
  • Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
  • Makiyayi Ya Kashe Abokai 2 A Nasarawa Kan Rikicin Kiwo
  • Jihar Kebbi Ta Kammala Shirye-shiryen Aikin Hajjin 2025
  • Hajjin 2025: An Fara Yi Wa Maniyyata Allurar Rigakafi A Jigawa
  • Jagora Ya Bada Umurnin A Gudanar Bincike Mai Zurfi A Fashewar Tashar Jiragen Ruwa Na Shaheed Rajae