Ofishin yada labarai na gwamnati a zirin Gaza ya sanar da cewa Falasdinawa kusan 300,000 da suka rasa matsugunansu ne suka koma gida a gabar tekun a ci gaba da aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wutar da aka cimma da kungiyar Hamas.

“Wannan ya zo ne bayan kwanaki 470 na kisan kiyashi da sojojin mamaya na Isra’ila suka yi,” in ji sanarwar, wanda ya yi sanadin shahadar Falasdinawa akalla 47,000 tare da lalata wargaza yankin Falasdinawan.

An bayyana cewa sama da kashi 90%, yankin ya lalace sakamakon hare haren Isra’ila.

An ruguza duk wasu wurare da cibiyoyi masu matukar mahimmanci kama daga asibitoci, makarantu, gidajen jama’a wuraren samar da ruwan sha da wutar lantarki.

A yanzu Falasdinawan dake komawa wannan yankin na da bukatar tallafin gaggawa musamman tantuna da wurin kwanci da ruwa mai tsafta da abinci da kula ta kiwon lafiya da dai sauransu inji kungiyoyin agaji.

“Muna kira ga al’ummomin kasa da kasa, kungiyoyin kasa da kasa da na Majalisar Dinkin Duniya, da kuma kasashen Larabawa dasu samar da wadanan kayayakin ga al’ummar falasdinu inji kungiyoyin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

Ba tare da nausawa daji ba, babban abin da ya kamata mu mayar da hankali a kai shi ne, mu fahimci sabubban da ke bayuwa zuwa ga afkuwar irin wadannan juye-juyen mulki a wannan nahiya tamu ta Afirka, a daya hannun kuma, gano dalilan da zai sanya a kauce musu, na da gayar muhimmanci. Sai dai, mu sani cewa; rashin daukar matakan kaucewa faruwar Juyin Mulkin, to fa tamkar guzurin tad-da shi ne, ko mun sani ko ba mu sani ba, musamman shugabanni, wadanda su ne ake tankwabe wani abu da suka fi kauna sama da komai cikin rayuwar duniya daga hannayensu, a halin suna numfashi ko akasin haka. Da farko ma tukuna, me ake nufi da juyin mulki?.

 

Ma’anar Juyin Mulki:

Ko mutum bai je makaranta ba, zai kai ga fahimtar juyin mulki na nufin tankwabar ko barar da gwamnati mai-ci ne, sawa’un, ta soja ce ko ta farar-hula. Ko a ilmance ma haka batun yake, wala’alla sai dan wasu karin bayani da za a iya samu. Ga wasu daga fassarorin masana game da hakikanin irin yadda za a kalli, ko fassara “juyin mulki” da; “wasu tsirarin mutane cikin gwamnati, su kifar da gwamnati mai-ci babu zato babu tsammani, a sau da yawan lokuta juyin mulkin kan afku ne cikin yanayi na gumurzu, kuma sau da yawa za a ga sojoji ne ke yin juyin tare da maye-gurbin manyan jagororin gwamnatin (da aka kifar) da wasu mutane na daban” (Decalo, 1990). A wata fassarar an ce, juyin mulki na nufin, “wani yunkuri ne karara da ya saba da tsarin mulkin kasa, wanda sojoji ko wasu manyan mutane cikin gwamnati ke yi na kifar da gwamnati mai-ci” (Powell & Thyne, 2011).

 

Rabe-raben Juyin Mulki:

Da yawan masana da masharhanta sun kasa juyin mulki zuwa gida hudu tare da gabatar da bayanansu daya bayan daya. Ga su kamar haka;

1- Kilasik Kuu “Classic Coup”.

2- Fales Kuu “Palace Coup”.

3- Kawunta Kuu “Counter Coup”, da kuma

4- Sibil-Militiri Kuu “Cibil-Military Coup”.

Akwai bukatar dan yin karin haske game da wadannan mabanbantan nau’o’i na juyin mulki hudu da aka lasafto:

 

Kilasik Kuu “Classic Coup

Yayin da sojoji suka game-baki tare da hambarar da wata gwamnati mai-ci, shi ake kira da Kilasik Kuu. Misali, a nan Nijeriya cikin shekarar 1983, inda sojojin wannan kasa suka hade-baki suka kifar da gwamnatin marigayi Alhaji Shehu Shagari, suka maye-gurbinsa da marigayi Janar Muhammadu Buhari.

 

Fales Kuu “Palace Coup

Yayin da wani sashe na jagororin mulki a kasa, suka tsige shugaban kasa ba tare da sun yi ittifaki da daukacin sojin kasar ba (face wasu tsirari daga cikinsu), shi ake kira Fales Kuu. Irin nau’in wannan juyin mulki, an yi shi a Kasar Mauritania, cikin shekarar 2008.

 

Kawunta Kuu “Counter Coup

Yayin da wasu suka yi juyin mulki, sai kuma wasu mutane daban suka sake yin wani juyin mulkin, don kalubalantar juyin mulkin farko, shi ake kira da Kawunta Kuu. Misali, bayan juyin mulkin da su Ironsi suka yi a Nijeriya cikin shekarar 1966, bayan wata shida kacal, sai wasu daga sojojin kasar suka hambarar da gwamnatin ta Aguiyi Ironsi.

 

Sibil-Militiri Kuu “Cibil-Military Coup

Yayin da sojoji da wasu daga cikin jama’ar gari ko ‘yan siyasa a kasa suka hade-baki wajen kifar da wata gwamnati mai-ci, shi ake kira da Sibil-Militiri Kuu. Irin wannan juyin mulki ne ya afku a Kasar Ghana cikin shekarar 1981, inda Jerry Rawlings ya hada-kai da wasu mutanen gari suka yi wa gwamnatin lokacin juyin mulki.

Sai dai, masana da sauran masharhanta na fadin cewa, yawancin juyin mulki na samar da canjin shugabanci ne kawai nan da nan, amma sai ya gadar da rashin kwanciyar hankali na tsawon lokaci a kasa. Ko a nan gida Nijeriya, za a ga cewa; tunanin da kabilar Ibo ke yi a yau cewa; an kange su ga barin samun damar shugabancin wannan kasa, na da alaka ta kud-da-kud da juyin mulki na farko da aka yi a kasar, shekara 51 da suka gabata, wanda sojoji “yan kabilar ta Ibo suka jagoranta. Bugu da kari, ana kallon juyin mulki da wata guguwa da ke barar da tsarin mulkin dimukradiyya, tare da yin silar samar da yanayi na take hakkin Dan’adam a kasa. Sannan, juyin mulkin, kan raunana karfin iko, ko ‘yancin gudanar da ayyukan da wasu hukumomi ke da shi, misali, bangaren shari’a. Juyin mulkin, kan jaza ci gaba da afkuwar wasu juyin mulkin a kasa daga lokaci zuwa lokaci.

Cikin lokuta da dama, za a ga jagororin juyin mulkin, na da’awar dawo da doka da oda ne a kasa tare da nuna cewa; za su zo da nagartattun tsare-tsare, don ciyar da kasa gaba, amma a karshen lamari, irin wadancan alkawura ba kasafai suke cikuwa ba.

Akwai ci gaba a mako na gaba inshaAllah.

 

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano November 2, 2025 Manyan Labarai Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima November 1, 2025 Manyan Labarai Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori November 1, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara
  • Dan Majalisar Jema’a/Sanga, Daniel Amos, Ya Koma Jam’iyyar APC
  • HKI Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza Inda Take Kashe Falasdinawa
  • Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta
  • Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan