Aminiya:
2025-11-03@08:50:49 GMT

Hadi Sirika ya ba wa kamfanin da bai cancanta ba kwangilar N2.8bn

Published: 28th, January 2025 GMT

Wani shaida ya bayyana wa kotu yadda tsohon Ministan Sufurin Jirgin Sama Sanata Hadi Sirika ya ba wa kamfanin da bai cancanta ba aikin gyaran Filin jirgin Katsina a kan Naira biliyan 2.8.

tsohon Daraktan Sayayya ne a ma’aikatar, Musa Obinyan ya bayyana wa kotu cewa a lokacin da Hadi Sirika yake ministan ba wa Kamfanin Al Buraq Investment Ltd, aikin gyaran filin jirgin, alhalin kamfanin bai cancanci a ba shi aikin ba.

Musa Obinyan ya shaida wa Babbar Kotun Abuja cewa rufa-rufa aka yi aka ba wa Al-Buraq, sannan nemo kuɗin aikin aka yi daga wani wuri aka biya.

Ya ba da shaida ne a ci gaba da sauraron shari’ar da Hukumar Yaƙi da Masu Karya Tattalin Arziƙin (EFCC) take tuhumar Hadi Sirika da badaƙalar Naira biliyan 19.4.

Da kuɗin hayar gidana da ke Kaduna nake sayen abinci a yanzu — Buhari ’Yan majalisa sun nemi cin hancin N480m kafin amincewa da kasafin jami’o’i —Bincike

Hukumar EFCC na zargin Hadi Sirika da laifuka 10 da suke da alaƙa da almundahana a lokacin da yake ministan sufurin jiragen sama.

Daga cikin laifukan, ana zargin tsohon, da ba da kwangila ga kamfanin Enginos Nigeria Ltd mallakin ƙaninsa, Abubakar Sirika.

Obinyan ya ƙara da cewa an sanya Alburak da Enginos a matsayin abubuwa daban-daban a kasafin ma’aikatar, amma daga bisani aka gano cewa bayanansu ɗaya a sashen sayen kayayyaki na ma’aikatar.

A baya an gurfanar da Hadi Sirika tare da ’yarsa Fatima Hadi Sirika, da surukinsa, Jalal Sule Hamma tare da kamfanin Al Buraq Global Investment Ltd.

Kotu ta ɗage shari’ar zuwa ranar 10 ga watan Maris, 2025.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Al Buraq kwangila

এছাড়াও পড়ুন:

Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa

Tsohuwar jarumar Kannywood, Mansurah Isa, ta ƙaryata labarin da wata jaridar intanet ta yaɗa cewa wai tana son ta auri shahararren dan TikTok, Ashiru Mai Wushirya, wanda ya yi tashe a kafafen sada zumunta a ’yan kwanakin nan.

A wani saƙo da ta wallafa, Mansurah ta ce labarin ƙarya ne kuma ya jefa ta da iyalinta cikin ruɗani da damuwa.

Ta ce, “Na shiga firgici bayan na ga wannan labarin. Ba ni da wata alaka da Mai Wushirya. Wannan sharri ne tsagwaron karya.”

Rahoton da aka yada a jaridar AMC Hausa ya yi iƙirarin cewa wai Mansurah ta ce ta shirya auren Mai Wushirya idan har yana son ta da gaske.

Kofin kofi mafi tsada a duniya ya shiga kasuwa a kan Naira miliyan 1.5m An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi

Amma jarumar ta yi watsi da wannan iƙirarin, tana mai cewa jaridar ta ɓata mata suna kuma ta karya ƙa’idojin aikin jarida.

Ta ce, “Na kira su, na ba su awa 24 su sauke labarin, amma har yanzu ba su yi hakan ba. Sun kira ni sun ba ni hakuri a waya, amma labarin har yanzu yana nan. Wannan abu ya zubar min da mutunci kuma ya saka iyalina cikin tashin hankali,” ina ji ta.

Mansurah ta bayyana cewa yanzu tana cikin shirin ‘WalkAwayCancer’, wani gagarumin shiri na wayar da kan jama’a kan mcutar daji, amma wannan labarin karya ya yi ƙoƙarin karkatar da hankalin mutane daga ainihin aikinta.

“Kun hana ni barci da kwanciyar hankali saboda labarin da babu gaskiya a cikinsa. Amma in sha Allahu, za ku ji daga gare mu,” in ji ta cikin fushi.

Har zuwa lokacin da muka kammala wannan labarin dai, kamfanin AMC Hausa bai fitar da wata sanarwa ba dangane da ƙarar da Mansurah ke shirin kai musu bisa zargin yaɗa labarin ƙarya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsagin Damagum da Anyanwu sun shirya mamaye hedikwatar PDP a yau
  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka
  • Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya 
  • Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya
  • Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini ba — Tinubu
  • Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa
  • Za mu ci gaba da shirye-shiryen babban taronmu — PDP