Hadi Sirika ya ba wa kamfanin da bai cancanta ba kwangilar N2.8bn
Published: 28th, January 2025 GMT
Wani shaida ya bayyana wa kotu yadda tsohon Ministan Sufurin Jirgin Sama Sanata Hadi Sirika ya ba wa kamfanin da bai cancanta ba aikin gyaran Filin jirgin Katsina a kan Naira biliyan 2.8.
tsohon Daraktan Sayayya ne a ma’aikatar, Musa Obinyan ya bayyana wa kotu cewa a lokacin da Hadi Sirika yake ministan ba wa Kamfanin Al Buraq Investment Ltd, aikin gyaran filin jirgin, alhalin kamfanin bai cancanci a ba shi aikin ba.
Musa Obinyan ya shaida wa Babbar Kotun Abuja cewa rufa-rufa aka yi aka ba wa Al-Buraq, sannan nemo kuɗin aikin aka yi daga wani wuri aka biya.
Ya ba da shaida ne a ci gaba da sauraron shari’ar da Hukumar Yaƙi da Masu Karya Tattalin Arziƙin (EFCC) take tuhumar Hadi Sirika da badaƙalar Naira biliyan 19.4.
Da kuɗin hayar gidana da ke Kaduna nake sayen abinci a yanzu — Buhari ’Yan majalisa sun nemi cin hancin N480m kafin amincewa da kasafin jami’o’i —BincikeHukumar EFCC na zargin Hadi Sirika da laifuka 10 da suke da alaƙa da almundahana a lokacin da yake ministan sufurin jiragen sama.
Daga cikin laifukan, ana zargin tsohon, da ba da kwangila ga kamfanin Enginos Nigeria Ltd mallakin ƙaninsa, Abubakar Sirika.
Obinyan ya ƙara da cewa an sanya Alburak da Enginos a matsayin abubuwa daban-daban a kasafin ma’aikatar, amma daga bisani aka gano cewa bayanansu ɗaya a sashen sayen kayayyaki na ma’aikatar.
A baya an gurfanar da Hadi Sirika tare da ’yarsa Fatima Hadi Sirika, da surukinsa, Jalal Sule Hamma tare da kamfanin Al Buraq Global Investment Ltd.
Kotu ta ɗage shari’ar zuwa ranar 10 ga watan Maris, 2025.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Sarki Sanusi II ya koka kan yawan cin bashin Najeriya
Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II ya koka bisa yawan bashin da Najeriya ke ciyowa da kuma yadda gwamnati ke facaka da kuɗaɗen.
Sarkin wanda tsohon Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN) ne, ya kuma bayyana cewa cire tallafin man fetur da Gwamnatin Tarayya ta yi shi ne mafi alheri, yana mai cewa da Gwamnatin ba ta cire tallafin mai ba, da Najeriya ta daɗe da tsiyacewa.
“Adawata a ɓangaren shan man ne, saboda muna ba da aikin yi ga matatun mai a Turai. Muna ba da aikin ga masu tace ɗanyen man,” in ji Sarki Sanusi.
Da yake jawabi a Taron Adabi na Duniya na Kano (KAPFEST) da aka gudanar a Kano ranar Asabar, masanin tattalin arzikin ya bayyana cewa ɗabi’ar yawan cin bashin Najeriya za ta yi mummunar illa ga tattalin arzikin ƙasar na tsawon lokaci.
Mutuwar majinyata: Asibitin Aminu Kano na roƙon KEDCO ya dawo da wutar lantarki Gidauniyar Misilli ta mayar da yara 150 makaranta a GombeMasanin tattalin arzikin ya bayyana damuwa musamman kan yadda gwamnati ke kashe kuɗaɗen da ta ciyo bashin.
Zuwa ƙarshen watan Maris, yawan bashin da ake bin Najeriya ya haura Naira tiriliyan 150.
A yayin taron wanda cibiyar Poetic Wednesdays Initiative (PWI), ta shirya, Sarki Sanusi II ya ce, ya ce, “Ina muke kai wannan tulin bashin da muke ciyowa a ƙasar nan?
“Zan yi farin cikin ganin an yi amfani da kuɗaɗen a fannin ilmantar da matasanmu, saboda su ne za su biya. Amma bai kamata mu yi ciyo bashi muna lafta wa tattalin arzikin ƙasa ba tare da zuba jari a fannin ilmantar da waɗanda su ne za su biya bashin ba.
“Nan da shekara 20 za mu faɗa a matsala a dalikin cin bashi. Dole a zuba jari a fannin inganta rayuwarsu domin samar da abubuwa.”
Ya bayyana cewa Najeriya ba ta yi sa’ar shugabanni nagari ba a tsawon lokaci, yana mai cewa yawancin shugabannin ƙasar ragwage ne masu yawan kawo uzuri.
Sarki Sanusi II ya bayyana kyakkyawan shugabanci a matsayin muhimmin abin da zai ceto Najeriya daga halin da take ciki, wanda ya kira na rashin sa’a.
Da yake sukar yanayin koma-bayan Najeriya alhali wasu ƙasashe sun yi gaba ta fannin kimiyya da fasaha da ci-gaban zamani, Sarki Sanusi II ya buƙaci matsala da su tashi domin karɓar ragamar shugabancin ƙasar, yana mai jaddada cewa hakan abu mai yiwuwa ne idan matasan suka jajirce.