Aminiya:
2025-11-02@18:12:57 GMT

Mutum 6 sun rasu yayin tsere wa ’yan bindiga a Sakkwato

Published: 24th, August 2025 GMT

Aƙalla mutane shida sun rasa rayukansu, yayin da har yanzu an nemi wasu uku an rasa, sakamakon kifewar kwale-kwale a Garin Faji na Ƙaramar Hukumar Sabon Birni da ke Jihar Sakkwato.

Lamarin ya faru ne lokacin da mazauna yankin ke tsere wa wani harin ‘yan bindiga da misalin ƙarfe 5:30 na safiyar Alhamis, 21 ga watan Agusta.

An tsinci gawar saurayi a gefen kudiddifi a Kalaba Sarkin Musulmi ya ayyana Litinin 1 ga watan Rabi’ul Awwal

Wannan shi ne karo na biyu cikin kasa da mako guda da irin wannan ibtila’i ya faru, domin a kwanaki shida da suka gabata, mutane huɗu sun mutu a hatsarin kwale-kwale makamancin wannan a Ƙaramar Hukumar Goronyo ta jihar.

Aminiya ta ruwaito cewa, waɗanda abin ya rutsa da su sun gaggauta shiga kwale-kwalen ne a ƙoƙarin tsere wa ‘yan bindigar da suka hango sun yi kwanton ɓauna.

Wani mazaunin garin da ya nemi a sakaya sunansa ya ce: “Saboda fargaba, mutane da yawa ba sa kwana a gidajensu. Sukan kwana a daji, sai safe su dawo gida. To, a ranar da abin ya faru, suna dawowa ne kwale-kwalen ya kife.”

Kazalika, wani mazaunin ya ce an shiga zaman ɗar-ɗar ne lokacin da suka hangi ‘yan bindigar na tunkaro su, lamarin da ya sa suka yi gaggawar shiga kwale-kwalen da ta kife a tsakiyar ruwa saboda an yi masa lodin da ya fi ƙarfinsa.

Ɗan majalisar dokokin Jihar Sakkwato mai wakiltar Sabon Birni, Hon. Aminu Boza, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce rashin tsaro ya tilasta mazauna da dama barin gidajensu suna kwana a jeji.

Ita ma Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Sakkwato (SEMA) ta tabbatar da faruwar hatsarin, wadda ta ce jami’inta sun ceto mutum 19 daga cikin ruwa, yayin da ake ci gaba da neman ragowar wasu mutum uku waɗanda suka ɓace.

Wannan mummunan lamari ya sake jaddada tsananin da mazauna Sakkwato ke ciki, inda wasu ƙauyuka suka zama kufai, yayin da ‘yan gudun hijira ke ƙaruwa sakamakon hare-haren ‘yan bindiga akai-akai.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Kwale kwale Sakkwato kwale kwale

এছাড়াও পড়ুন:

Barcelona ta shiga zarwacin Victor Osimhen

Kungiyar ƙwallon ƙafa ta Barcelona da ke Sipaniya na ƙoƙarin ɗauko Victor Osimhen a matsayin wanda zai maye gurbin Robert Lewandowski wanda ke fama da matsalar raunuka

Ɗan jaridar ƙasar Sifaniya, Gabriel Sans na Mundo Deportivo ya bayyana cewar, Barcelona na neman wanda zai maye gurbin Robert Lewandowski a matsayin mai jefa ƙwallo a raga, hakan ne ya sa ƙungiyyar ta amince da ɗaukar Osimhen.

’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA

A ƙarshen kakar bana ne ake tunanin up Lewandowski zai bar Barca, wanda zai tilasta wa ƙungiyyar neman wani zaƙaƙurin ɗan wasan gaba mai ciyo ƙwallo.

Victor Osimhen dai a bazarar nan ne ya koma Galatasaray bayan barin Napoli ta Italiya.

Osimhen dai ba ya ɓoye aniyarsa ta buga wasa a ɗaya daga cikin manyan gasannin Nahiyyar Turai biyar ba, ciki har da Firimiya ta Ingila da LaLiga ta Sifaniya, inda Barcelona ke cikin manyan ƙungiyoyin gasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
  • Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Barcelona ta shiga zarwacin Victor Osimhen
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m
  • An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku
  • ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara