Aminiya:
2025-11-03@01:58:56 GMT

Gwamnatin Sakkwato ta bai wa ’yan gudun hijira tallafin kuɗi da shinkafa

Published: 5th, September 2025 GMT

Bayan sama da shekaru biyu a kan mulki, gwamnatin Sakkwato ta fara waiwayar ’yan gudun hijira da hare-haren ’yan bindiga suka raba da muhallansu.

A dukkanin ƙananan hukumomi 23 na jihar akwai ’yan gudun hijira da ke buƙatar ɗauki.

Tsohon mataimakin Gwamnan Gombe da wasu jiga-jigai sun fice daga PDP zuwa APC Saudiyya ta ƙaƙaba wa masu laifukan rashin ɗa’a sabuwar tara

Wasu ma sun tsallaka zuwa Jamhuriyar Nijar, inda suka yada zango a jihohin Dosso, Maradi da Tahoua.

Mutane da dama, musamman yara, suna cikin mawuyacin hali.

Wasu marayu suna yin sana’o’i kamar tuƙa baro, tara dutse ko yin bara domin samun abin ci, ba tare da wata kulawa daga gwamnati ba.

Da yawa daga cikinsu ba sa zuwa makaranta saboda yunwa da rashin tallafi.

A ƙoƙarin samar wa waɗanda suka rasa ’yan uwa a hare-haren baya-bayan nan, gwamnatin Sakkwato ta raba tallafin Naira miliyan 69.75 da buhun shinkafa 210 ga iyalan waɗanda abin ya shafa a Kware da Gwadabawa.

Gwamna Ahmad Aliyu, ya bayyana hare-haren a matsayin abin baƙin ciki, inda ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da tallafa wa jami’an tsaro da kuma kare al’ummar jihar.

Ya nuna damuwa kan yadda wasu ke bai wa ’yan bindiga bayanai, wanda hakan ke kawo rashin tsaro.

Dangane da rabon tallafin, gwamnati ta ce duk wanda ya rasa ɗan uwansa zai samu Naira miliyan biyu da buhun shinkafa biyar.

Waɗanda suka samu rauni za su karɓi Naira dubu 250 da buhunan shinkafa uku.

A Kware an kashe mutane 22, a Gwadabawa kuwa mutane 11 ne suka rasu, yayin da wasu 11 suka ji rauni.

Ana sa ran wannan tallafi zai zagaya sauran ƙananan hukumomin jihar, tare da ƙarin tallafi ga dubban ’yan gudun hijira da ke buƙatar taimako.

 

Ga hotunan yadda rabon tallafin ya gudana:

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan gudun hijira gwamnati Sakkwato yan gudun hijira

এছাড়াও পড়ুন:

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Wasanni Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar? November 2, 2025 Wasanni Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025? November 1, 2025 Wasanni Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Karamar Hukumar Bubura Ta Kai Tallafin Kayayyakin Abinci Cibiyar Gyaran Hali
  • Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara
  • Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma
  • Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai