An kama mace ɗauke da bindiga da N2m a otal
Published: 5th, September 2025 GMT
Rundunar ’yan sandan Jihar Kogi ta kama wata budurwa mai suna Charity Williams ’yar shekaru 23, wadda aka same ta da kuɗi Naira miliyan 2,047.500 da miyagun ƙwayoyi da kuma bindigar fistol.
A cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar, ta ce jami’anta da ke aiki da sashin Okene a Ƙaramar hukumar Okene a jihar, sun kama wanda ake zargin a wani otal da ke Okene.
Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan Jihar (PPRO), William Aya, ya ce bayan da aka samu labarin, jami’ansu sun kai farmaki otal ɗin tare da kama matar.
Aya ta ce babban wanda ake zargin kan lamarin wani ne mai suna Christopher Kadiri da ya tsere.
“A wani samame da jami’an tsaro na rundunar ’yan sandan Najeriya reshen Okene suka kai, sun kama Charity Williams, mai shekara 23, tare da ƙwato bindiga ƙirar fistol guda ɗaya, da kuɗi Naira miliyan 2,047,300 da harsashi na nau’in 9mm guda shida, muggan ƙwayoyi, gatari da wayoyin salula huɗu.
“Wannan ya biyo bayan bayanan sirri na cewa, an ga wani da ake zargi da aikata laifi a Yuwander Lodge a maɓoyar masu aikata laifi ne a ƙauyen Oguda, Okene.
“Nan take ’yan sanda suka kutsa kai cikin masaukin, bayan da suka binciki ɗaya daga cikin ɗakunan da wani Christopher Christopher Kadiri ya nema, wata mace mai suna Charity Williams mai shekara 23, an kama su kuma an ƙwato abubuwan da ke zargi a ɗakin,” in ji sanarwar.
Ya ce, ana ci gaba da ƙoƙarin cafke duk waɗanda ake zargin gaba ɗaya, yayin da ake ci gaba da bincike.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
“Haka kuma an kama wata mata mai shekaru 34 da ake zargi da hannu a lamarin, tare da wasu masu gidan marayu guda biyu da ke Abuja da Jihar Nasarawa, inda aka gano wasu yaran da ake kyautata zaton an yi safarar su. Wasu daga cikin gidajen marayun da aka gano ana amfani da su ne a matsayin cibiyoyin ajiye yara, inda ake jiran ‘kwace’ ko sayar da su da sunan daukar nauyin marayu.”
Ya ce, “An gano gidajen marayu guda hudu da ke Kaigini, Kubwa Edpressway Abuja; Masaka Area 1, Mararaba kusa da Abaca Road; da kuma Mararaba bayan Kasuwar Duniya suna da alaka da wannan kungiya, kuma ana ci gaba da bincike a kansu.”
Ya kara da cewa, daya daga cikin masu korafin ya bayyana cewa ya biya Naira miliyan 2.8 a matsayin kudin daukar yaro, sannan ya biya Naira 100,000 a matsayin kudin shawara ga daya daga cikin ‘yan kungiyar.
Sanarwar ta kara da cewa, “Wani mai korafi ya ce shi ma ya biya Naira miliyan 2.8 kudin daukar yaro da Naira 100,000 kudin shawara ga wani dan kungiyar.
“An canza sunayen yawancin yaran da aka ceto, lamarin da ya kara wahalar da bincike da gano asalinsu,” in ji sanarwar.
Darakta Janar ta NAPTIP, Binta Adamu Bello, ta bayyana damuwarta kan wannan lamari, inda ta ce safarar yara ta zama babbar matsala a kasa.
Ta hanyar Adekoye, DG din ta nuna damuwa game da yadda wasu gidajen marayu ke amfani da raunin jama’a wajen aiwatar da safarar yara.
Ta ce, “Abin takaici ne yadda wasu masu mugunta da ke da sunayen kwararru da matsayi a cikin al’umma, suke amfani da matsayin su wajen yaudarar mutanen da ke cikin mawuyacin hali, su yi safarar ‘ya’yansu, da dama daga cikinsu ma sun tsira ne daga halaka a lokacin rikice-rikicen al’umma ko na manoma da makiyaya, sannan a sayar da su ga iyaye masu neman haihuwa a matsayin daukar yaro ba tare da sahihin izinin iyayensu ba.
“Wannan abin ba za a yarda da shi ba, kuma wadanda aka kama kan wannan mugun aiki za su fuskanci hukuncin doka yadda ya kamata.
“’Ya’yanmu ba kayayyaki ba ne da za a ajiye su a gidajen marayu a sayar ga mai biyan mafi tsada. Wannan dole ya tsaya,” in ji ta.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA