Aminiya:
2025-09-17@23:11:55 GMT

Simon Ekpa: An ɗaure ɗan Nijeriya kan laifin ta’addanci a Finland

Published: 1st, September 2025 GMT

Wata kotu a ƙasar Finland ta yanke wa ɗan Najeriya mai rajin ɓallewar ƙasar Biyafara, Simon Ekpa, hukuncin ɗaurin shekara shida a gidan yari bisa laifukan da suka shafi ta’addanci, zamba da karya doka.

Kotun ta tabbatar da cewa Ekpa ya aikata laifuka da suka haɗa da ƙoƙarin hargitsa jama’a da nufin ta’addanci da kuma shiga cikin ayyukan ƙungiyoyin masu ɗaukar makami.

An kashe mutum 5 an sace limamai da hakimi a Sakkwato Gwamnan Neja ya rushe kwamishinoninsa

Haka kuma, kotun ta ce an same shi da laifin zamba ta haraji da keta wasu dokokin Finland.

A cewar kotun, daga watan Agusta 2021 zuwa Nuwamba 2024, Ekpa ya yi amfani da kafafen sada zumunta wajen yaɗa shirye-shiryen neman ɓallewar Biyafara daga Najeriya, da kuma ingiza mabiyansa su aikata laifuka.

Rahoton kotun ya ce ƙungiyoyin da yake jagoranta sun kafa wasu tsageru masu ɗaukar makami, waɗanda aka bayyana a matsayin ƙungiyoyin ta’addanci. Har ila yau, an tabbatar da cewa ya samar musu da makamai, harsasai da abubuwa masu fashewa ta hannun wasu mabiyansa.

An ce duk waɗannan ayyukan Ekpa ya ke gudanarwa ne daga garin Lahti na ƙasar Finland, duk da cewa shi ya musanta zarge-zargen a kotu.

Sai dai alƙalin ya bayyana cewa hukuncin ba shi ne na ƙarshe ba, inda ake tsammanin Ekpa zai iya ɗaukaka ƙara zuwa kotu mafi girma.

Martanin Gwamnatin Najeriya

Bayan yanke hukuncin, Gwamnatin Tarayya ta bayyana jin daɗinta, tana mai cewa wannan hukunci “babban lamari ne” wajen tabbatar da adalci da kuma ƙarfafa dangantaka tsakanin Najeriya da Finland.

A wata sanarwa da Ministan Yaɗa Labarai, Mohammed Idris, ya fitar a ranar Litinin, ya ce: “Tsawon wasu shekaru wutar da Ekpa ya rura ta haddasa bala’i kan rayukan ɗaruruwan ‘yan Najeriya.

“Iyalai sun tarwatse, kasuwanci sun lalace, yara sun zama marayu, al’umma kuma sun riƙa rayuwa cikin tsoro.

“Saboda haka wannan hukuncin ya tabbatar da matsayar da Najeriya ta riƙa, tare da nuna wa masu tsattsauran ra’ayi cewa duniya na kallonsu, kuma doka za ta cim musu.”

Ya ƙara da cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu za ta ci gaba da kare mutuncin Najeriya da ɗaukakar ‘yan ƙasa ta kowace fuska—ta hanyar diflomasiyya, soja, shari’a da sauran hanyoyin da suka dace.

Ministan ya kuma yi kira ga duk wanda ya bi hanyar Ekpa ko sauran masu tayar da zaune tsaye su ajiye makami ya rungumi zaman lafiya, yana mai cewa: “Najeriya ƙasa ce mai faɗi, kuma za ta iya ɗaukar kowa, amma ba a samun ci gaba a kowace al’umma da ke fuskantar tashin hankali da rarrabuwar kawuna.”

A ƙarshe, gwamnatin ta gode wa ofishin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, rundunar soji, ’yan sanda da sauran hukumomin tsaro, bisa jajircewa wajen kare ƙasar daga duk wani ƙalubale.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Biyafara tabbatar da

এছাড়াও পড়ুন:

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

Ya ce kuma kayan da ake fitarwa zuwa waje waɗanda ba man fetur yanzu su kusa yin kai da kai da fetur.

Ya ƙara da cewa ajiyar kuɗaɗen ƙasar a waje ya haura kusan dala biliyan 42, daga biliyan 32 lokacin da Tinubu ya hau mulki.

Har ila yau, ya ce an biya bashin da ya haura biliyan bakwai, ciki har da miliyan 800 da ake bin jiragen saman Nijeriya.

Fadar Shugaban Ƙasa ta ce yanzu jihohi na iya biyan albashi da fansho a kan lokaci, sannan suna da rarar kuɗi don ayyukan raya ƙasa, abin da ba a saba gani ba a baya.

“Bayan shekara biyu da watanni biyar kacal a ofis, Shugaba Tinubu ya cimma abubuwa da dama. Ko da Atiku da magoya bayansa ba su yadda ba, ’yan Nijeriya suna ganin sauyin,” in ji Onanuga.

Fadar Shugaban Ƙasa ta kuma zargi Atiku da jam’iyyar PDP da yaɗa maganganun da za su kawo tashin hankali.

Ya bayyana cewa yawancin matsalolin da ake fuskanta sun samo asali ne daga rashin kyakkyawan shugabanci tun a lokacin PDP, lokacin da Atiku yake mataimakin shugaban ƙasa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • Microsoft ya ƙwace shafukan wasu kamfanoni 340 a Najeriya
  • Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa