ASUU: Malaman Jami’ar FUK sun yi zanga-Zanga kan rashin cika musu alƙawura
Published: 27th, August 2025 GMT
Ƙungiyar Malaman Jami’a (ASUU) reshen Jami’ar Tarayya Kashere (FUK), ta yi zanga-zangar lumana, inda ta buƙaci Gwamnatin Tarayya ta aiwatar da yarjejeniyar da suka yi da sauran buƙatunsu da ba a cika ba.
Zanga-zangar ta fara ne daga ofishin ƙungiyar, ta bi ta ginin shugaban jami’ar, sannan ta ƙare a bakin ƙofar shiga makarantar.
Shugaban ASUU na jami’ar, Dakta Shehu El-Rasheed, ya ce gwamnati ta kasa cika alƙawuran da suka jawo yajin aikin watanni takwas a shekarar 2022.
Ya ce har yanzu ba a biya malamai albashin baya ba, haka kuma babu ƙarin albashi na tsawon shekaru.
Ya ja hankalin gwamnati cewa hakan na iya haifar da damuwa a harkar ilimi a jami’ar.
Wani malami, Dakta Muhammad Sheriff Ramadan, ya ce ƙarancin albashi na tilasta wa malamai yin wasu ayyuka don samun ƙarin kuɗin shiga.
Ya buƙaci gwamnati ta ƙara albashi domin inganta rayuwarsu da harkar ilimi.
Wasu ɗaliban jami’ar, Dung Hannatu Yakubu da Precious Moses Ayomide, sun bayyana fargabarsu cewa rashin jituwar ASUU da gwamnati na iya jawo tsaikon karatu da kuma ƙara musu shekaru kafin kammala karatunsu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jami ar Kashere yarjejeniya
এছাড়াও পড়ুন:
Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar
Gwamna Inuwa ya kuma jaddada bukatar bin ka’idojin kariya a harkokin sufurin ruwa, inda ya yi kira ga shugabannin kananan hukumomi, da shugabannin al’umma, da direbobin kwale-kwale da hukumomin da ke da ruwa da tsaki da sauran wadanda suka dace su kara kaimi wajen ganin ana kiyaye duk ka’idojin kariya don magance sake afkuwar ibtila’in a nan gaba.
Ya umurci Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Jiha (SEMA) da Majalisar. Karamar Hukumar Nafada su bayar da duk wani tallafin da ya dace ga iyalan da abin ya shafa tare da hada hannu da hukumomin da abin ya shafa don inganta tsaro da wayar da kan al’ummomin da ke yankunan kogi.
Gwamna Inuwa Yahaya ya yi addu’a yana mai cewa “A madadin gwamnati da al’ummar Jihar Gombe, ina mika sakon ta’aziyyarmu ga iyalan mamatan tare da addu’ar Allah ya jikansu da rahama ya gafarta musu kurakuransu, ya kuma saka musu da Aljannar Firdaus”.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA