Aminiya:
2025-07-23@23:34:46 GMT

Tsohon Alkalin Alkalan Najeriya, Lawal Uwais ya rasu

Published: 6th, June 2025 GMT

Tsohon Alkalin Alkalan Najeriya, Mohammed Lawal Uwais ya rasu yana da shekaru 89 a duniya.

Mmarigayin, wanda ya kasance Alkalin Alkalan na tsawon shekaru 11 daga 1995 zuwa 2006 ya rasu ne a Abuja ranar Juma’a.

Mun gurfanar da mutum 29 a kotu kan zargin kashe DPO a Kano – ’Yan sanda Wani mutum ya mutu a cikin rijiya a Kano

Wata majiya daga iyalan mamacin ta tabbatar da rasuwar sannan ta ce shirye-shirye sun kankama na yi wa mamacin jana’iza.

An dai haifi marigayin ne a ranar 12 ga watan Yunin 1936 a Zariyan jihar Kaduna.

A zamanin da yake shugabancin Alkalan, ya kawo sauye-sauyen shari’a da dama musamman a bangaren fadada harkokin siyasa, inda hakan ya zama silar yi wa jam’iyyu da dama rajista a Najeriya.

Kazalika a shekara ta 2007, kuma jagoranci kwamitin yi wa harkokin zaben Najeriya kwaskwarima wanda tsohon Shugaban Kasa, marigayi Umaru Musa ’Yar’aduwa ya naɗa shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yar aduwa Lawal Uwais

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’an tsaro sun dakile yunkurin Sanata Natasha na shiga harabar Majalisa

Jami’an tsaro sun hana Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan da ’yan rakiyarta shiga haramar Majalisar Dokoki ta Kasa, inda ta je da niyyar halartar zaman Majlasiar Dattawa a ranar Talata.

Jami’an tsaro a daukacin kofofin shiga harabar majalisar sun hana ta shiga harabar majalisar ne a lokacin da ta yi yunkurin shiga domin halartar zaman ranar Talata, a yayin da magoya bayanta suka rako ta domin nuna goyon bayansu gare ta kan dakatarwar da majalisar ta yi mata.

A watan Maris ne da Majalisar Dattawa ta dakatar da Sanata Natasha na tsawon wata shida kan zargin rashin da’a da kuma rashin bin tsarin wurin zaman da aka tanadar da mambobin majalisar a ranar 20 ga watan Fabrairu, 2025.

A kana haka ne ’yar majalisar mai wakiltar Kogit ta Tsakiya ta garzaya Babbar Kotun Abuja, wadda ta umarci majalidar ta dawo da Sanata Natasha, bisa hujjar cewa majailsar ta wuce gona da iri wajen dakatar da ita har na tsawon wata shida.

Kamfanonin lantarki za su katse wuta kan bashin N5.2trn da suke bin gwamnati  An wajabta wa ɗaliban firamare mallakar lambar NIN a Bauchi

Alkalin kotu, Mai Shari’a Binta Nyako, ya bayyana cewa hukuncin da majalisar ta yanke ya yi tsauri da yawa, kuma ba shi da mazauni a doka.

Ta bayyana cewa doka na bukatar majalisar ta zauna sau 181 ne a shekara, kuma dakatarwar ta kusa tsawon wadanan kwanaki.

Ta ce hakan na nufin al’ummarta za su shafe kusan shekara guda ba tare mai wakiltans su ba a zauren majalisar, kuma ya saba da dokar kasa.

Tun loakcin Natasha ke ta kokarin komawa bakin aiki, inda a ranar Asabar ta lashi takobin halartar zama a ranar Talatar nan, idan majalisar ta dawo daga hutu.

Amma a ranar Litinin Shguaban Kwamitin Sadarwa na Majalisar Dattawa, Sanata Yemi Adaramodu ya fitar da sanarwa yana gargadin ta da cewa ya nisanci majalsiar.

Adaramodu ya yi ikirarin cewa Natasha ba ta cika umarnin kotu na biyan tarar Naira miliyan biyar ga Gwamnatin Tarayya kan kan raina kotu ba, da kuwa wallafa sakon neman afuwa a manyan jaridu biyu da kuma shafinta na Facebook.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kaddamar Da Bikin BIRTV2025 A Beijing
  • Matasa 3 sun rasu yayin wanka a rafi a Bauchi
  • Makarantun Kano Za Su Fara Hutun Ƙarshen Zango A Ranar Juma’a – Gwamnati
  • DAGA LARABA: Abubuwan da ya kamata yara su yi yayin hutun makaranta
  • Jami’an tsaro sun dakile yunkurin Sanata Natasha na shiga harabar Majalisa
  • NAJERIYA A YAU: Yadda tsadar taki ke hana noman masara da shinkafa
  • Mutum 16 sun mutu a haɗarin jirgin sama a Bangladesh
  • Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
  • Kasar Sin Na Fatan EU Za Ta Yi Aiki Da Ita Bisa Alkibla Guda Da Tsara Hadin Gwiwa Na Shekaru 50 Masu Zuwa
  • An kaddamar Da Wani Shiri Na Ba ‘Yan Mata 200,000 Tallafin Audugar Mata A Kano