Tsohon Alkalin Alkalan Najeriya, Lawal Uwais ya rasu
Published: 6th, June 2025 GMT
Tsohon Alkalin Alkalan Najeriya, Mohammed Lawal Uwais ya rasu yana da shekaru 89 a duniya.
Mmarigayin, wanda ya kasance Alkalin Alkalan na tsawon shekaru 11 daga 1995 zuwa 2006 ya rasu ne a Abuja ranar Juma’a.
Mun gurfanar da mutum 29 a kotu kan zargin kashe DPO a Kano – ’Yan sanda Wani mutum ya mutu a cikin rijiya a KanoWata majiya daga iyalan mamacin ta tabbatar da rasuwar sannan ta ce shirye-shirye sun kankama na yi wa mamacin jana’iza.
An dai haifi marigayin ne a ranar 12 ga watan Yunin 1936 a Zariyan jihar Kaduna.
A zamanin da yake shugabancin Alkalan, ya kawo sauye-sauyen shari’a da dama musamman a bangaren fadada harkokin siyasa, inda hakan ya zama silar yi wa jam’iyyu da dama rajista a Najeriya.
Kazalika a shekara ta 2007, kuma jagoranci kwamitin yi wa harkokin zaben Najeriya kwaskwarima wanda tsohon Shugaban Kasa, marigayi Umaru Musa ’Yar’aduwa ya naɗa shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yar aduwa Lawal Uwais
এছাড়াও পড়ুন:
Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara
Ɗan takarar jam’iyyar Labour a zaɓen shugaban ƙasa na 2023, Peter Obi, ya ziyarci tsohon shugaban ƙasa, Olusegun Obasanjo, da kuma sabon Olubadan na Ibadan, Rashidi Ladoja, a wani zagayen ganawa da manyan ’yan siyasa gabanin zaɓen 2027.
Obi, wanda ke ƙoƙarin ƙara yauƙaƙa zumunci da manyan shugabanni a fadin ƙasar, ya bayyana cewa ziyarar na da alaƙa da burinsa na ganin an samu shugabanci na gaskiya da riƙon amana a Najeriya.
An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wutaA wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, Obi ya bayyana cewa ziyararsa ta musamman zuwa Ibadan na da nufin girmama Rashidi Ladoja, wanda aka naɗa a matsayin Olubadan, da kuma jaddada muhimmancin Ibadan a siyasa, zamantakewa, da tattalin arzikin ƙasar.
“Na kai ziyara don girmama sabon Olubadan, Rashidi Ladoja, wanda ƙwarewarsa a matsayin tsohon sanata, gwamna, kuma attajiri za ta taimaka wajen ɗaga martabar Ibadan,” in ji Obi.
Ya ƙara da cewa tattaunawarsa da Obasanjo da Ladoja na da nasaba da ci gaban Najeriya da kuma shugabanci da ke da burin sauya al’umma ta fuskar gaskiya da adalci.
Ziyarar Obi na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da shirye-shiryen siyasa gabanin babban zaɓen shekarar 2027, inda ake hasashen zai sake tsayawa takarar shugaban ƙasa.