HausaTv:
2025-06-06@20:31:03 GMT

Rasha Ta Kai Munanan Hare-hare A Kasar Ukiraniya

Published: 6th, June 2025 GMT

Rasha ta yi amfani da makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuki wajen kai hare-hare a kan birnin Kiev da kuma wasu gundumomi 9 na kasar.

Rundunar sojan saman kasar Ukiraniya ta ce; Kasar tasu ta fuskanci munanan hare-hare da makamai masu linzami a cikin gundumomin gabashi, yammaci da kuma babban birnin kasar Kiev.

Rundunar soja da take tafiyar da sha’anin Mulki a birnin Kiev ta sanar da cewa; Daga cikin wuraren da aka kai wa hare-haren da akwai tashar jirgin kasa, hakan nan kuma muhimman cibiyoyi da gidajen fararen hula.

Magajin birnin Vitali Klitschko ya sanar da cewa; Mutum daya ya rasa ransa yayin da wasu mutane 20 su ka jikkata sanadiyyar harin na Rasha. Haka nan kuma gobara ta tashi lokacin da makamai masu linzami da jirage marasa matuki su ka fada a cikin unguwanni 3 na birnin.

A can kasar Rasha kuwa, an sanar da kakkabo jirage uku marasa matuki da Ukiraniya ta harba wa birnin Moscow, haka nan an dakatar da kai da komowar jirage a filiyen jiragen sama na birnin Moscow, da kuma Caloga.

Sai dai kuma wata majiyar a Rasha ta ce gobara ta tashi a cikin wani gida a garin Ingilz, saboda fadawa jirgin sama maras matuki akansa.

Yaki dai ya barke ne a tsakanin Rasha da Uniraniya tun a ranar 24 ga watan Febrairu 2022, wanda ya zuwa yanzu ya ci rayukan mutane 12,000 kamar yadda MDD ta ambata.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

Har ila yau, ya bayyana cewa, bangaren tekun kudancin kasar Sin gaba daya yana cikin kwanciyar hankali kuma babu wata matsala game da ‘yancin zirga-zirgar jiragen ruwa da na sama da dukkan kasashe ke morewa bisa doka.

Ya ce, a ko da yaushe, kasar Sin na dagewa kan amfani da tattaunawa da tuntubar juna wajen warware sabani da magance abubuwan da aka sha bamban a kai game da teku yadda ya kamata a tsakanin kasashen da abin ya shafa kai-tsaye, bisa mutunta hakikanin tarihi na gaskiya.

Haka nan, ya kamata kasashen da ba na yankin ba su mutunta kokarin da kasashen yankin suke yi na tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a tekun kudancin kasar Sin, maimakon haddasa fitina da haifar da zaman doya da manja. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Beirut: HKI Ta Kai Hare-hare A Unguwar Dhahiya Dake Birnin Beirut
  • Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai
  • Sojoji sun dakile hare-haren ‘Yan Boko Haram biyu a Borno
  • Shugaban Kasar Rasha Vladimir Putin Zia Kawo Ziyara Tehran Nan Kusa
  • Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba
  • Jami’an Tsaron A Nan Iran Sun Kama Yan Kungiyar ISIS Kafin Su Aiwatar Da Hare-Hare
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kai Hare-Hare Kan Yankunan Siriya Musamman Yankin Kudancin Kasar
  • Medvedev : babu makawa Rasha za ta mayar da martani mai zafi ga hare-haren kyiv