Rasha Ta Kai Munanan Hare-hare A Kasar Ukiraniya
Published: 6th, June 2025 GMT
Rasha ta yi amfani da makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuki wajen kai hare-hare a kan birnin Kiev da kuma wasu gundumomi 9 na kasar.
Rundunar sojan saman kasar Ukiraniya ta ce; Kasar tasu ta fuskanci munanan hare-hare da makamai masu linzami a cikin gundumomin gabashi, yammaci da kuma babban birnin kasar Kiev.
Rundunar soja da take tafiyar da sha’anin Mulki a birnin Kiev ta sanar da cewa; Daga cikin wuraren da aka kai wa hare-haren da akwai tashar jirgin kasa, hakan nan kuma muhimman cibiyoyi da gidajen fararen hula.
Magajin birnin Vitali Klitschko ya sanar da cewa; Mutum daya ya rasa ransa yayin da wasu mutane 20 su ka jikkata sanadiyyar harin na Rasha. Haka nan kuma gobara ta tashi lokacin da makamai masu linzami da jirage marasa matuki su ka fada a cikin unguwanni 3 na birnin.
A can kasar Rasha kuwa, an sanar da kakkabo jirage uku marasa matuki da Ukiraniya ta harba wa birnin Moscow, haka nan an dakatar da kai da komowar jirage a filiyen jiragen sama na birnin Moscow, da kuma Caloga.
Sai dai kuma wata majiyar a Rasha ta ce gobara ta tashi a cikin wani gida a garin Ingilz, saboda fadawa jirgin sama maras matuki akansa.
Yaki dai ya barke ne a tsakanin Rasha da Uniraniya tun a ranar 24 ga watan Febrairu 2022, wanda ya zuwa yanzu ya ci rayukan mutane 12,000 kamar yadda MDD ta ambata.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ba zai yiwu mu bar Khamenei a raye ba — Isra’ila
Ministan Tsaron Isra’ila, Israel Katz ya ce ba zai yiwu su bar jagoran addinin Iran, Ayatollah Ali Khamenei a raye ba.
Israel Katz ya yi barazana ga Ayatollah yana mai cewa ya zama tilas ya ɗauki alhakin hare-hare da makamai masu linzami da Iran ta yi a kan wata cibiyar lafiya da ke kusa da Tel Aviv.
Hisbah ta lalata katan 243 na barasa da wasu kayan maye a Yobe Guguwar ruwan sama ta yi ɓarna a Kwalejin Kimiyya da Fasaha a KogiKafin harin an yi ƙoƙari kwashe marasa lafiya da dama, saboda a ceto rayukansu.
Tuni dai Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ziyarci Cibiyar Lafiya ta Soroka da ke Beersheba da harin makami mai linzami na Iran ya faɗawa.
Sai dai ita kuma Iran din ta ce ta kai harin ne kan sansanin sojoji da ke kusa da asibitin.
Kalaman Mista Katz na nuna cewa sojojin Isra’ila a yanzu za su yi ƙoƙarin ganin sun kashe Ayatollah — bayan kashe kwamandojinsa na soji da dama.
A makon da ya gabata ne Isra’ila ta ƙaddamar da hare-hare ta sama kan babbar abokiyar gabarta a yankin Gabas ta Tsakiya Iran, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar manyan kwamandojin sojin ƙasar, tare da lalata wasu cibiyoyin nukiliyata da kuma kashe fararen hula da dama.