Leadership News Hausa:
2025-06-06@18:00:17 GMT

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Published: 6th, June 2025 GMT

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Bugu da kari, Xi Jinping ya jaddada cewa, ya kamata kasar Amurka ta daidaita matsayinta kan batun Taiwan da idon basira, kada masu neman raba yankin Taiwan daga kasar Sin su tura Amurka da Sin cikin rikici.

A nasa bangare, shugaba Trump na Amurka ya ce, yana matukar girmama shugaba Xi Jinping, kuma huldar dake tsakanin Amurka da Sin tana da muhimmanci.

Ya ce kasar Amurka ta yi farin cikin ganin karuwar tattalin arzikin kasar Sin. Kana, hadin gwiwar dake tsakanin Amurka da Sin za ta ba da gudummawa ga kasa da kasa. Ya ce a nan gaba kuma, kasarsa za ta ci gaba da bin manufar kasar Sin kasa daya tak a duniya. Bugu da kari, ya ce kasashen biyu sun samu nasarar tattaunawar tattalin arizki da cinikayya a birnin Geneva, inda suka kuma cimma kyakkyawar yarjejeniyar. Kasar Amurka tana fatan hadin gwiwa da kasar Sin wajen aiwatar da yarjejeniyar, haka kuma tana maraba da zuwan daliban kasar Sin.

Kaza lika, shugaba Xi ya yi maraba da Donald Trump ya sake kawowa kasar Sin ziyara, inda shi kuma shugaba Trump ya bayyana godiyarsa matuka. Daga bisani, shugabannin biyu sun cimma matsaya daya kan ci gaba da aiwatar da ra’ayi daya da aka cimma a birnin Geneva, yayin gudanar da sabon zagayen taron tattaunawa. (Mai Fassara: Maryam Yang)

 

 

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Afirka Tana Shirin Samar Da Maganin Kwalara Da Kanta

Shugabannin nahiyar Afirka sun tattauna hanyoyin samar da maganin kwalara a cikin nahiyar.

An tattauna wannan batun ne dai a yayin taron da aka yi ta hanyar bidiyo daga nesa akan hanyoyin magance cutuka mabanbanta da su ka hada da riga-kafi.

Wadanda su ka halarci tattaunawar ta bidiyo sun hada shugabannin kasashen Angola, Namibia, Malawi da kuma DRC.

Shugaban kasar  Zambia Hakayinde Hichilema  ya bayyana cewa; Da akwai bukatar nahiyar Afirka ta fara samar da magunguna cikin gaggawa tare da dogaro da nahiyar wajen samar da kudaden da ake bukata domin yin hakan, saboda kaucewa dogaro da waje.”

Haka nan kuma shugaban kasar ta Zambia ya ce: Saboda kwalara idan ta barke ba ta san iyakar kasashe ba, ya kamata mu yi aiki tare da kuma samar da tsarin yin gargadi na gaggawa a tsakanin kasashen makwabta.”

Shi kuwa shugaban kasar Angola João Lourenço, wanda kuma shi ne yake rike da kambun jagorancin kungiyar nahiyar Afirka, ya bayyana cewa: ” Cutar kwalara ta fi karfin a dauke ta a matsayin wani yanayi na gaggawa da yake bijirowa a fagen kiwon lafiya, tana a matsayin kaulabale ne  mai girma dake hana ci gaba na tattalin arziki da bunkasar al’umma a nahiyar ta Afirka.”

Shi kuwa shugaban hukumar lafiya ta duniya : Adhanom Gibisos cewa ya yi; A cikin wannan shekarar ta 2025 a cikin nahiyar Afirka ne za yi kaso 1/3 na dukkanin kwalarar da za ta barke a duniya, kuma a cikin nahiyar ne dai za a sami mutuwar kaso 99% na jumillar wadanda cutar za ta kaseh a duniya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Afirka Tana Shirin Samar Da Maganin Kwalara Da Kanta
  • Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
  • Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai
  • Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore
  • Shugaban Kasar Iran Ya Tattauna Ta Wayar Tarko Da Tokwaransa Na Masar Da Saudiya
  • Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin
  • Shugaba Tinubu Ya Karrama Bill Gates Da Lambar Girmamawa Ta CFR
  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Cewa: Amurka Da Isra’ila Suna Da Mugun Nufi Kan Iran Da Kasashen Musulmi
  • Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva