Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Published: 6th, June 2025 GMT
Bugu da kari, Xi Jinping ya jaddada cewa, ya kamata kasar Amurka ta daidaita matsayinta kan batun Taiwan da idon basira, kada masu neman raba yankin Taiwan daga kasar Sin su tura Amurka da Sin cikin rikici.
A nasa bangare, shugaba Trump na Amurka ya ce, yana matukar girmama shugaba Xi Jinping, kuma huldar dake tsakanin Amurka da Sin tana da muhimmanci.
Kaza lika, shugaba Xi ya yi maraba da Donald Trump ya sake kawowa kasar Sin ziyara, inda shi kuma shugaba Trump ya bayyana godiyarsa matuka. Daga bisani, shugabannin biyu sun cimma matsaya daya kan ci gaba da aiwatar da ra’ayi daya da aka cimma a birnin Geneva, yayin gudanar da sabon zagayen taron tattaunawa. (Mai Fassara: Maryam Yang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya
An gudanar da taron tattaunawa na duniya kan kirkire-kirkire da bude kofa da ci gaba na bai daya, jiya Juma’a a birnin Lagos na Nijeriya. Yayin taron wanda babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin CMG da karamin ofishin jakadancin Sin dake Lagos suka shirya, ministan kula da harkokin matasa na Nijeriya Ayodele Olawande da shugaban CMG Shen Haixiong, sun gabatar da jawabai ta kafar bidiyo.
A cewar ministan na Nijeriya, cikin shekaru 5 da suka gabata, dubban matasan kasar sun ci gajiyar tallafin karatu da shirye-shiryen horo da na musaya da Sin ta samar, kuma wannan hadin gwiwa da ake yi a aikace ya kara fahimta da aminci tsakanin kasashen biyu. Ya kara da cewa, a shirye ma’aikatarsa take ta karfafa hadin gwiwa da sassa masu ruwa da tsaki na kasar Sin wajen ci gaba da fadada shirye-shiryen musaya da na hadin gwiwa da suka shafi matasa.
A nasa bangare, Shen Haixiong ya ce a matsayinta na babbar kafar yada labarai dake watsa shirye shiryenta ga sassa daban daban na duniya, tashar talabijin ta CCTV dake karkashin CMG da abokan huldarta, za su yayata shawarar Sin ta jagorantar harkokin duniya da gabatar da tafarkin Sin na zamanantar da kanta da karfinta na kirkire kirkire a sabon zamani ga al’ummar duniya. (Mai fassara: FMM)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA