Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Published: 6th, June 2025 GMT
Bugu da kari, Xi Jinping ya jaddada cewa, ya kamata kasar Amurka ta daidaita matsayinta kan batun Taiwan da idon basira, kada masu neman raba yankin Taiwan daga kasar Sin su tura Amurka da Sin cikin rikici.
A nasa bangare, shugaba Trump na Amurka ya ce, yana matukar girmama shugaba Xi Jinping, kuma huldar dake tsakanin Amurka da Sin tana da muhimmanci.
Kaza lika, shugaba Xi ya yi maraba da Donald Trump ya sake kawowa kasar Sin ziyara, inda shi kuma shugaba Trump ya bayyana godiyarsa matuka. Daga bisani, shugabannin biyu sun cimma matsaya daya kan ci gaba da aiwatar da ra’ayi daya da aka cimma a birnin Geneva, yayin gudanar da sabon zagayen taron tattaunawa. (Mai Fassara: Maryam Yang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Hare-haren Benuwe: Tinubu ya ziyarci waɗanda suka jikkata a asibiti
Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, ya kai ziyara Jihar Benuwe domin jajanta wa mutanen jihar bisa hare-haren da suka faru a wasu ƙauyuka kwanan nan.
Ya je ne domin nuna alhininsa ga waɗanda abin ya shafa da kuma tattaunawa da shugabanni don nemo mafita mai ɗorewa.
Mun shirya yin sulhu da ’yan bindiga — Gwamnatin Sakkwato Sojoji sun raunata shugaban ISWAP na Najeriya, AlbarnawiA yayin ziyarar tasa ta yini guda, Shugaba Tinubu ya fara ne da ziyartar Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jihar Benuwe, inda ta duba waɗanda suka jikkata.
Shugaban ya shirya ganawa da iyalan waɗanda aka kashe, da waɗanda suka rasa muhallansu, da kuma shugabannin al’umma.
Hakazalika, Shugaba Tinubu zai gana da manyan masu ruwa da tsaki s jihar, ciki har da sarakunan gargajiya, ’yan siyasa, shugabannin addinai, da ƙungiyoyin matasa.
Burinsa shi ne samo hanyar kawo ƙarshen rikicin da ya addabi yankunan Yelwata, Apa, da kuma Agatu.
Yadda rikicin ya samo asaliRikicin a Jihar Benuwe ya daɗe ana tafka shi, kuma mafi yawan lokuta rikici ne tsakanin manoma da makiyaya.
Manoma na zargin cewa shanun makiyaya na lalata gonakinsu, yayin da makiyaya ke kukan rashin wuraren kiwo.
A watan Afrilun shekarar 2023, sama da mutum 50 ne suka rasa rayukansu a ƙauyen Umogidi da ke Ƙaramar Hukumar Otukpo.
A watan Yunin 2023 kuma, an kai farmaki ƙauyuka da dama a Guma da Logo, inda mutane da dama suka mutu.
An daɗe ana zargin wasu daga cikin hare-haren ƙungiyar Miyetti Allah da wasu ’yan bindiga ne ke kai wa.
Yawancin mutane sun rasa gidajensu da gonakinsu, wasu kuma sun tsere zuwa sansanonin ’yan gudun hijira.
Duk da irin ƙoƙarin da gwamnonin da suka gabata suka yi, har yanzu matsalar na ci gaba da faruwa.
Ziyarar Shugaba Tinubu tana ƙarfafa wa mutane gwiwa cewa za a iya samo mafita domin kawo ƙarshen kashe-kashen da ke faruwa a Benuwe da sauran wuraren da rikicin ya shafa.