Leadership News Hausa:
2025-06-19@18:42:53 GMT

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Published: 6th, June 2025 GMT

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Bugu da kari, Xi Jinping ya jaddada cewa, ya kamata kasar Amurka ta daidaita matsayinta kan batun Taiwan da idon basira, kada masu neman raba yankin Taiwan daga kasar Sin su tura Amurka da Sin cikin rikici.

A nasa bangare, shugaba Trump na Amurka ya ce, yana matukar girmama shugaba Xi Jinping, kuma huldar dake tsakanin Amurka da Sin tana da muhimmanci.

Ya ce kasar Amurka ta yi farin cikin ganin karuwar tattalin arzikin kasar Sin. Kana, hadin gwiwar dake tsakanin Amurka da Sin za ta ba da gudummawa ga kasa da kasa. Ya ce a nan gaba kuma, kasarsa za ta ci gaba da bin manufar kasar Sin kasa daya tak a duniya. Bugu da kari, ya ce kasashen biyu sun samu nasarar tattaunawar tattalin arizki da cinikayya a birnin Geneva, inda suka kuma cimma kyakkyawar yarjejeniyar. Kasar Amurka tana fatan hadin gwiwa da kasar Sin wajen aiwatar da yarjejeniyar, haka kuma tana maraba da zuwan daliban kasar Sin.

Kaza lika, shugaba Xi ya yi maraba da Donald Trump ya sake kawowa kasar Sin ziyara, inda shi kuma shugaba Trump ya bayyana godiyarsa matuka. Daga bisani, shugabannin biyu sun cimma matsaya daya kan ci gaba da aiwatar da ra’ayi daya da aka cimma a birnin Geneva, yayin gudanar da sabon zagayen taron tattaunawa. (Mai Fassara: Maryam Yang)

 

 

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Hare-haren Benuwe: Tinubu ya ziyarci waɗanda suka jikkata a asibiti 

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, ya kai ziyara Jihar Benuwe domin jajanta wa mutanen jihar bisa hare-haren da suka faru a wasu ƙauyuka kwanan nan.

Ya je ne domin nuna alhininsa ga waɗanda abin ya shafa da kuma tattaunawa da shugabanni don nemo mafita mai ɗorewa.

Mun shirya yin sulhu da ’yan bindiga — Gwamnatin Sakkwato Sojoji sun raunata shugaban ISWAP na Najeriya, Albarnawi

A yayin ziyarar tasa ta yini guda, Shugaba Tinubu ya fara ne da ziyartar Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jihar Benuwe, inda ta duba waɗanda suka jikkata.

Shugaban ya shirya ganawa da iyalan waɗanda aka kashe, da waɗanda suka rasa muhallansu, da kuma shugabannin al’umma.

Hakazalika, Shugaba Tinubu zai gana da manyan masu ruwa da tsaki s jihar, ciki har da sarakunan gargajiya, ’yan siyasa, shugabannin addinai, da ƙungiyoyin matasa.

Burinsa shi ne samo hanyar kawo ƙarshen rikicin da ya addabi yankunan Yelwata, Apa, da kuma Agatu.

Yadda rikicin ya samo asali

Rikicin a Jihar Benuwe ya daɗe ana tafka shi, kuma mafi yawan lokuta rikici ne tsakanin manoma da makiyaya.

Manoma na zargin cewa shanun makiyaya na lalata gonakinsu, yayin da makiyaya ke kukan rashin wuraren kiwo.

A watan Afrilun shekarar 2023, sama da mutum 50 ne suka rasa rayukansu a ƙauyen Umogidi da ke Ƙaramar Hukumar Otukpo.

A watan Yunin 2023 kuma, an kai farmaki ƙauyuka da dama a Guma da Logo, inda mutane da dama suka mutu.

An daɗe ana zargin wasu daga cikin hare-haren ƙungiyar Miyetti Allah da wasu ’yan bindiga ne ke kai wa.

Yawancin mutane sun rasa gidajensu da gonakinsu, wasu kuma sun tsere zuwa sansanonin ’yan gudun hijira.

Duk da irin ƙoƙarin da gwamnonin da suka gabata suka yi, har yanzu matsalar na ci gaba da faruwa.

Ziyarar Shugaba Tinubu tana ƙarfafa wa mutane gwiwa cewa za a iya samo mafita domin kawo ƙarshen kashe-kashen da ke faruwa a Benuwe da sauran wuraren da rikicin ya shafa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Na Son Taka Rawar Gani Wajen Maido Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Sauri
  • Kotun Amurka ta daure ’yan Najeriya 5 shekaru 159 kan aikata damfara
  • Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital
  • Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Sakamakon Ziyarar Shugaba Xi A Kazakhstan
  • Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne – Obasanjo
  • Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
  • Hare-haren Benuwe: Tinubu ya ziyarci waɗanda suka jikkata a asibiti 
  • Xi Da Shugabannin Kasashe 5 Na Tsakiyar Asiya Sun Halarci Bikin Rattaba Hannu
  • Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53
  • Shugaba Xi Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan Kassym-Jomart Tokayev