HausaTv:
2025-07-24@03:37:11 GMT

Oman ta mika wa Iran takardun shawararin Amurka game da tattaunawar nukiliya

Published: 1st, June 2025 GMT

Iran ta tabbatar da cewa ta samu shawarar da Amurka ta gabatar mata daga hannun kasar Oman game da shirin nukiliyar kasar na zaman lafiya da ake tattaunawa a kai.

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araghchi ya tabbatar da cewa Iran ta samu wani bangare na shawarwarin daga Amurka daga Oman mai shiga tsakani kan batun a wani sakon da ya wallafa a shafinsa na X.

Ya karbi sakon ne daga hannun takwaransa na Oman Badr Albusaidi, wanda ya gudanar da wata gajeriyar ziyara a Tehran.

Saidai ministan harkokin wajen Iran din bai bayyana abinda shawarwarin ke kunshe da ba, amma ya jaddada cewa za a duba su a kuma mayar da amsa wacce ta yi daidai da muradin kasar da kuma hakkokin al’ummar Iran.

Har ila yau, a ranar Asabar, Araghchi ya sake jaddada ‘yancin Jamhuriyar Musulunci ta Iran na inganta sinadarin Uranium don zaman lafiya, yana mai cewa hakki ne na kasa da ba za a iya tattaunawa a kai ba.

Tun a watan Afrilu ne dai Iran da Amurka suka faro tattaunawa a shiga tsakanin kasar Oman a kokarin warware sabanin dake tsakanin bangarorin biyu dama wasu kasashen yammacin duniya kan shirin nukiliyar iran na zaman lafiya.

Kasashen dai na zargin Iran da kokarin mallakar makamman kare dangi batun da Iran ke musantawa tana mai cewa shirinta na lumana ne.

Amurka dai na son Iran ta rage inganta sinadarin uranium din ta zuwa “sifili.” Abinda iran ke cewa ba zai yi wu ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ministocin Tsaron kasashen Rasha Da JMI Sun Hadu A Birnin Mosco

Ministocin tsaro na kasar Rasha ta JMI sun hadu a birnin Mosco don tattauna batun karfafa dangantakar tsaro a tsakaninsu a dai dai lokacinda al-amuran tsaro suke kara tabarbarewa a yankin kudancin Asiya.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto jakadan kasar Iran a Mosco yana fadar haka.

Kazem Jalali, ya bayyana cewa kasashe biyu suna kara zurfin dangantakarsu da juna a dai-dai kasashen biyu suke kara fuskantar matsinn lamba daga kasashen yamma musamman Amurka, da kuma HKI.

Kasashen biyu sun ga yakamata su kara dankon zumunci a tsakaninsu a fagen tsaro, bayan yakin kwanaki 12 wanda Amurka da HKI suka dorowa kasar Iran.

A wannan zuwan dai ministan tsaron JMI ya raka Dr Ali Larijani babban mai bawa jagoran juyin njuya hali musulunci shawara a ganawarsa da shugaba Vladmir Putin a fadar Krimlin a ranar Lahadi.

Kazem Jalali, ya bayyana cewa a wannan karon ma bangarorin biyu sun tattauna baton karfafa dangantakar tsaron kasashen biyu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran: Sojojin Ruwan Iran Sun Kori Jirigin Yakin Amurka Daga Tekun Oman
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Jaddada Hakkinta Na Tace Sinadarin Uranium A Cikin Kasarta
  • Shugaban Amurka Trump Ya Bukaci Gurfanar Da Tsohon Shugaban Amurka Barack Obama A gaban Kuliya
  • Pezeshkian: Tunanin Kawo Karshen Shirin Nukiliyar Iran Ya Yi Kama Da Tabuwa
  • Trump ya fitar da Amurka daga UNESCO saboda amincewa da  Falasdinu a matsayin Mamba
  • Hana Natasha Zaman Majalisa Barazana Ne Ga Dimokuraɗiyya — CLO
  • Fizishkiyan: Batun Kare Hakkin Bil’adama Ba Komai Ba Ne Sai Karya
  • Wata Kungiyar Ta Bukaci Shugaban Kasa Ya Cika Alkwarin Marigayi Shugaba Buhari Game Da Shehu Usman Aliyu Shagari
  • Jami’in Shari’ar Kasa Da Kasa Ya Bayyana Cewa: Harin Da Aka kai Kan Iran Babban Laifi Ne
  • Ministocin Tsaron kasashen Rasha Da JMI Sun Hadu A Birnin Mosco