Shugaban Nijar Janar Abdourahmane Tiani ya ce har yanzu ana wa kasarsa zagon kasa ta fuskar tsaro musamman daga kasashen yamma.

Janar Tiani ya ambato kasar Faransa da tsohuwar gwamnatin Amurka a matsayin wadanda ke da hannu a matsalolin tsaro da ake fama da su.

Ya bayyana hakan ne a wata hira ta musamman da gidan talabijin na kasar RTN da aka watsa a yammacin ranar Asabar.

Ya dai yi bayyani ne kan batutuwa daban daban ciki har da halin da kasar ke ciki.

Shugaban kasar ta Nijar, ya kuma jinjinawa sojojin kasar dake bakin daga domin tsare kasar dare da rana, ya kuma isar da ta’aziyya ga sojojin da suka rasa rayukansu a kokarin kare kasar daga sha’anin ta’addanci.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

Kafar CGTN ta kasar Sin ce ta wallafa binciken jin ra’ayin jama’ar kan dandalolin harsunan turancin Ingilishi, da Sifaniyanci, Faransanci, da Larabci, da harshen Rasha, inda masu bayyana ra’ayoyi 6,886 daga sassan kasashen ketare daban daban suka bayyana ra’ayoyinsu cikin sa’o’i 24. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sabon Firay Ministan Sudan Ya Bukaci Kasashen Dake Taimaka Wa “RSF” Da Su Daina
  • Sabon Fira Ministan Sudan Ya Bukaci Kasashen Dake Taimaka Wa “RSF” Da Su Daina
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Yana Ziyarar Aiki A Kasar Masar, inda Ya Gana Da Shugaban Kasar
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hare-Hare Kan Filin Jirgin Saman Ben Gurion A Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Araghchi zai fara ziyarar kwanaki biyu a kasashen Masar da Lebanon
  • Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ta Iran Ya Ce: Taron Kungiyar BRICS Zai Kawo Bunkasar Tattalin Arziki
  • Oman ta mika wa Iran takardun shawararin Amurka game da tattaunawar nukiliya
  • Macron : Faransa za ta iya sanya takunkumi ga gwamnatin Isra’ila matukar ba ta kawo karshen killace Gaza ba