Nijar : Kasashen Faransa da Amurka ne ke kitsa mana hare-haren ta’addanci
Published: 1st, June 2025 GMT
Shugaban Nijar Janar Abdourahmane Tiani ya ce har yanzu ana wa kasarsa zagon kasa ta fuskar tsaro musamman daga kasashen yamma.
Janar Tiani ya ambato kasar Faransa da tsohuwar gwamnatin Amurka a matsayin wadanda ke da hannu a matsalolin tsaro da ake fama da su.
Ya bayyana hakan ne a wata hira ta musamman da gidan talabijin na kasar RTN da aka watsa a yammacin ranar Asabar.
Ya dai yi bayyani ne kan batutuwa daban daban ciki har da halin da kasar ke ciki.
Shugaban kasar ta Nijar, ya kuma jinjinawa sojojin kasar dake bakin daga domin tsare kasar dare da rana, ya kuma isar da ta’aziyya ga sojojin da suka rasa rayukansu a kokarin kare kasar daga sha’anin ta’addanci.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”
Kafar CGTN ta kasar Sin ce ta wallafa binciken jin ra’ayin jama’ar kan dandalolin harsunan turancin Ingilishi, da Sifaniyanci, Faransanci, da Larabci, da harshen Rasha, inda masu bayyana ra’ayoyi 6,886 daga sassan kasashen ketare daban daban suka bayyana ra’ayoyinsu cikin sa’o’i 24. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp