Kungiyar Hamas wacce take iko da zirin gaza ta bukaci masu shiga tsakanin Amurkawa su ngamtar da ita kan cewa HKI zata dakatar da yaki ta kuma fice daga zirin gaza. Amma shawarar da Steve Witkoff ya gabatar bata kunshi wani abu wanda zaia gamsar da kungiyar ta amince da wani sulhu ba.

Jihad Taha kakakin kungiyar ya bayyana cewa Hamas tana nazarin shawarar da Witskoff ya gabatar da tsagaita wuta a gaza wanda ya amince da dakatar da wuta na wucin gadi sannan a sake komawa yaki da kuma shigo a kayakin agaji.

Y ace shawarar bata ambaci ficewar sojojin HKI daga yankin ba.

Taha ya bayyana cewa shawarar bata da wani abin dogaro wanda Hamas da kungiyoyin masu gwagwarmaya zasu riki na tsagaita wuta a gaza. Amma dukm da haka suna nazarinsa kuma zasu bayyana ra’yinsu nan gaba.

Ya Zuwa yanzu dai sojojin yahudawan sun kashe Falasdinawa fiye da 54000 a cikin shekara da rabi da suke fafatawa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gaza : Sabon kisan kiyashi a kusa da wurin rarraba kayan abinci

Jami’ai a Falasdinu sun ce akalla mutum 31 ne sukayi shahada sannan wasu sama da 150 sun jikkata, bayan wani hari da Isra’ila ta kai kusa da wurin rabon abinci a birnin Rafah.

Dama shugaban hukumar MDD da ke kula da yan gudun hijirar Falasdinawa, Philippe Lazzarini, ya ce rabon kayan agajin ya zama tarkon mutuwa.

Lamarin dai ya faru ne a kusa da wata cibiyar rarraba kayan abinci da gidauniyar agaji ta Gaza (GHF) ke gudanarwa, wani kamfani mai zaman kansa da ke samun goyon bayan Isra’ila da Amurka da kungiyoyin agaji na kasa da kasa suka yi suka.

Kakakin kungiyar Hamas Sami Abu Zohri yayi Allah wadai da gwamnatin Isra’ila kan harin da ta aikata a rabon kayan agaji a Gaza, Inda ya jaddada cewa an yi wannan kisan kiyashi ne tare da goyon bayan Amurka.

Dangane da wannan kisan kiyashi da zubar da jinin shahidai, ya yi kira ga dukkanin al’ummar musulmi da masu son ‘yanci a fadin duniya da su tashi tsaye wajen yakar masu kisan gillar da sahyoniyawa ke yi.

A wani share kuma kungiyar gwagwarmayar Falasdinawan ta yi kira ga Majalisar Dinkin Duniya, da cibiyoyinta, musamman ma kwamitinta na tsaro, da su dauki matakan da suka dace don tilastawa gwamnatin Isra’ila ta kawo karshen zubar da jini da take yi, tare da gaggauta bude mashigar Zirin da aka yi wa kawanya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gaza : Sabon kisan kiyashi a kusa da wurin rarraba kayan abinci
  • MDD : Gaza na cikin bala’i mafi muni tun soma yaki a Zirin a Oktoban 2023
  • Limamin Sallar Juma’ar Tehran Ya Jaddada Cewa: Babu Wanda Zai Dakatar Da Iran Tace Sinadarin  Uranium
  • ‘Yan Gwagwamayar Falasdinu Sun Halaka Sojojin Mamayar Isra’ila Masu Yawa A Wani Harin Kwanton Bauna
  • Macron : Faransa za ta iya sanya takunkumi ga gwamnatin Isra’ila matukar ba ta kawo karshen killace Gaza ba
  • Hana shigar da abinci da Isra’ila ta yi zuwa Gaza ‘laifi ne na yaki’: MDD
  •  DRC: Joseph Kabila Ya Bayyana A Yakin Dake Karkashin Kungiyar M23
  • Yemen: Matukar Gaza Tana Fuskantar Yaki, To Babu Tsaro A HKI
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Aiwatar Da Kisan Kiyashi Kan Falasdinawa A Yankin Zirin Gaza