Ɓarawo ya haɗiye ɗan kunnen Naira biliyan ɗaya
Published: 6th, April 2025 GMT
Jami’an tsaro sun jiran kayan ado na ’yan kunnayen zinare su wuce ta na’urar binciken fasinjan jirgin sama kafin a gano kayan da aka sace a hukumance.
An kama wani mutum mai shekara 32, mai suna Jaythan Lawrence Glider bisa zargin satar ’yan kunne biyu na zinare na sama da Dala Amurka 769,000 kwatankwacin Naira biliyan 1 da miliyan 177 dubu dari 615 da 840 daga wani babban kantin da ke Millenia a birnin Orlando da ke Jihar Florida a Amurka a ranar 26 ga Fabrairu.
A cewar sashen ’yan sanda na Orlando, Glider ya dauki matakin da ba a saba gani ba na haɗiye ’yan kunnayen da ya sace.
A cewar rahoton ’yan sanda da kafar yada labarai ta WFLA, Glider ya yi amfani da damar shiga sashen kayan ado masu tsada a kantin Tiffany & Co a ranar 26 ga Fabrairu ta hanyar nuna matsayin wakilin ɗan wasan ƙwallon kwando na Orlando Magic.
Rahotanni sun ce wannan dabarar ta ba shi damar shiga cikin sashen manyan kayayyaki masu tsada, inda ya yi awon gaba da su.
An kai shi kurkuku bayan an tsayar da motarsa a kan hanyar Interstate 10 a gundumar Washington.
An kama shi ne bisa zargin kin amincewa da kama shi, baya ga wasu fitattun sammaci guda 48 da aka gano daga Colorado.
Al’amura sun zama abin mamaki lokacin da Glider ya tambayi ma’aikatan gidan yarin, “Shin za a tuhume ni da abin da na hadiye?”
Wannan shigar da bincike da aka yi ya kai ga duba jikin mutumin, inda aka gano wasu abubuwan da hadiya a cikinsa.
Hukumomin sun yi zargin cewa, waɗannan ’yan kunnayen da aka sace, waɗanda darajarsu ta kai Dalar Amurka 769,000 (kwatankwacin Naira biliyan 1 da miliyan 177 dubu dari 615 da 840), inda aka yi zargin Glider ya haɗiye.
Jami’an tsaro a yanzu suna jiran gano kayan ta hanyar na’urar bincike.
Kamar yadda aka sani, haɗiye ƙananan abubuwa kamar ’yan kunnaye bai fiya haifar da babbar illa ba.
A cewar ƙwararrun likitocin, idan abin ya gaza inci ɗaya ko kuma ƙasa da inci 2, to zai iya wucewa ta hanji ba tare da haifar da wata matsala ba.
Glider yana da tarihin matsalolin shari’a, inda aka ba shi sammaci guda 48 a Colorado musamman ma, an kuma tuhume shi da laifin yin fashi a wani kantin Tiffany & Co da ke Texas a cikin shekarar 2022.
Bayan kama shi a baya-bayan nan, Glider na fuskantar tuhumar babbar sata a matakin farko da fashi da abin rufe fuska.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
An gano gawar mutum 15 bayan hatsarin kwalekwale a Neja
An gano gwawar mutum 15 a yayin da ake ci gaba neman wasu uku bayan hastarin kwalekwale da ya auku a yankin Ƙaramar Hukumar Shiroro da ke Jihar Neja.
Kwalekwalen ya kife ne a yayin da yake ɗauke da mutum 43 da buhuna 60 na shansherar shinkafa da shanu uku da tumaki biyu a ranar Asabar.
Kifewar kwalekwalen ta auku ne a sakamakon karonsa da wani kututture bayan ya ɗauki fasinjojin daga yankin Guni zai kai su kasuwar mako-mako da ke yankin Zumba da ke Ƙaramar Hukumar Shiroro.
Manajan Hukumar Albarkatun Koguna ta Ƙasa (NIWA), mai kula da yankin, Akapo Adeboye, ya ce an gano gwawar mutum 15, amma ana ci gaba neman wasu mutum uku, ko da yake cewa an yi nasarar ceto mutum 26 da ke sanye da rigunan kariya da ransu, bayan aukuwar hatsarin.
HOTUNA: Yadda Aisha ta koma gidan Buhari na Kaduna NAJERIYA A YAU: Matakan Da Muke Dauka Don Karfafawa ’Yan Najeriya Kwarin Gwiwar Kada Kuri’a —INECAdebayo ya bayyana cewa, “Mutanen sun taso ne daga ƙauyen Shayita za su tafi Kasuwar Kwata da ke Zumba tare da kayansu na miliyoyin kuɗaɗe a ranar Asabar 26 ga watan Yuli, 2025.
“Jami’an NIWA sun gudanar da aikin ceto, amma an samu asarar rayuka 18, an ceto wasu 26, kuma aka ci gaba da aiki da kuma ƙoƙarin kamo mai kwalekwalen.”
Shaidu sun ce hastarin ya faru ne da misalin ƙarfe biyu na ranar Asabar, kuma yawancin fasinjojin mata ne da ƙananan yara, kuma jami’an Hukumar Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA) sun tabbatar da hakan.
Sarkin Ruwan Zumba, Umar Isah, ya ce mutum 15 ne suka rasu, an ceto 25, amma an yi asarar shanu uku da buhu 60 na shansherar shinkafa.
“A cikin mutum 15 da suka rasu har da ƙananan yara uku mata da gano gawarwakinsu,” in ji shi.
Amma Darakta Janar na Hukumar NSEMA, Abdullahi Baba Arah, ya ce gawa 13 aka gano kuma an yi jana’izarsu a ranar Lahadi.
Arah, wanda ya tabbatar da asarar wasu mutane da dabbobi da kayan abinci a hatsarin, ya ce gawarwakin sun haɗa da mata takwas da maza uku da kuma yara biyu.