Aminiya:
2025-09-17@23:24:12 GMT

Ɓarawo ya haɗiye ɗan kunnen Naira biliyan ɗaya

Published: 6th, April 2025 GMT

Jami’an tsaro sun jiran kayan ado na ’yan kunnayen zinare su wuce ta na’urar binciken fasinjan jirgin sama kafin a gano kayan da aka sace a hukumance.

An kama wani mutum mai shekara 32, mai suna Jaythan Lawrence Glider bisa zargin satar ’yan kunne biyu na zinare na sama da Dala Amurka 769,000 kwatankwacin Naira biliyan 1 da miliyan 177 dubu dari 615 da 840 daga wani babban kantin da ke Millenia a birnin Orlando da ke Jihar Florida a Amurka a ranar 26 ga Fabrairu.

A cewar sashen ’yan sanda na Orlando, Glider ya dauki matakin da ba a saba gani ba na haɗiye ’yan kunnayen da ya sace.

A cewar rahoton ’yan sanda da kafar yada labarai ta WFLA, Glider ya yi amfani da damar shiga sashen kayan ado masu tsada a kantin Tiffany & Co a ranar 26 ga Fabrairu ta hanyar nuna matsayin wakilin ɗan wasan ƙwallon kwando na Orlando Magic.

Rahotanni sun ce wannan dabarar ta ba shi damar shiga cikin sashen manyan kayayyaki masu tsada, inda ya yi awon gaba da su.

An kai shi kurkuku bayan an tsayar da motarsa a kan hanyar Interstate 10 a gundumar Washington.

An kama shi ne bisa zargin kin amincewa da kama shi, baya ga wasu fitattun sammaci guda 48 da aka gano daga Colorado.

Al’amura sun zama abin mamaki lokacin da Glider ya tambayi ma’aikatan gidan yarin, “Shin za a tuhume ni da abin da na hadiye?”

Wannan shigar da bincike da aka yi ya kai ga duba jikin mutumin, inda aka gano wasu abubuwan da hadiya a cikinsa.

Hukumomin sun yi zargin cewa, waɗannan ’yan kunnayen da aka sace, waɗanda darajarsu ta kai Dalar Amurka 769,000 (kwatankwacin Naira biliyan 1 da miliyan 177 dubu dari 615 da 840), inda aka yi zargin Glider ya haɗiye.

Jami’an tsaro a yanzu suna jiran gano kayan ta hanyar na’urar bincike.

Kamar yadda aka sani, haɗiye ƙananan abubuwa kamar ’yan kunnaye bai fiya haifar da babbar illa ba.

A cewar ƙwararrun likitocin, idan abin ya gaza inci ɗaya ko kuma ƙasa da inci 2, to zai iya wucewa ta hanji ba tare da haifar da wata matsala ba.

Glider yana da tarihin matsalolin shari’a, inda aka ba shi sammaci guda 48 a Colorado musamman ma, an kuma tuhume shi da laifin yin fashi a wani kantin Tiffany & Co da ke Texas a cikin shekarar 2022.

Bayan kama shi a baya-bayan nan, Glider na fuskantar tuhumar babbar sata a matakin farko da fashi da abin rufe fuska.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 

Yarjejeniyar, a cewar daukacin mahalarta taron, ta nuna wani gagarumin mataki na kawo karshen tashe-tashen hankula, garkuwa da mutane da satar shanu a Arewa maso Yamma, da kuma yankin Arewa.

 

Yarjejeniyar wacce Mai Maradin Katsina da Hakimin Kurfi, Alhaji Mansur Amadu Kurfi, da shugaban karamar hukumar, Babangida Abdullahi Kurfi suka shirya, ta gudana ne a dajin Wurma, inda ake fama da rashin tsaro.

 

Manyan jagororin ‘yan bindigan da suka hada da Alhaji Usman Kachalla Ruga da Sani Muhindinge da Yahaya Sani (Hayyu) da kuma Alhaji Shu’aibu duk sun yi alkawarin tsagaita wuta.

 

Daga baya suka sako mutanen da suka kama kuma suka bar manoma su koma gonakansu ba tare da wata barazana ba.

 

Sai dai kasa da wata guda da kulla yarjejeniyar, an tattaro cewa ‘yan bindigar sun sake kai hari a Zamfara inda suka yi awon gaba da masallata da dama.

 

Wata majiya ta cikin garin, ta shaida cewa, harin ya afku ne a lokacin sallar asuba da misalin karfe 5:30 na safe, inda ‘yan bindigar suka afkawa masallacin, suka kewaye shi, sannan suka tattara masallatan zuwa daji.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar