Aminiya:
2025-06-15@11:13:05 GMT

Abin da ya sa ba ma cin naman Akuya — Fulani

Published: 6th, April 2025 GMT

Binciken da Jaridar Aminiya ta gudanar ya nuna cewa, wasu Fulani daga Karamar Hukumar Jahun ta Jihar Jigawa sun yi imani cewa, idan suka ci naman akuya, maza za su kamu da cututtukan da suka shafi maraina, musamman ciwon mara da aka fi sani da ƙaba ko kumburin maraina, yayin da mata kuma za su kamu da ƙuraje a fatar jikinsu.

Malam Aminu Muhammad Jahun ya shaida wa wakilinmu cewa, tun yana yaro yake guje wa cin naman akuya, yana mai bayyana cewa, yawancin Fulani a yankinsu ba sa cin naman akuya, kuma idan aka ci, za a kamu da ciwon ƙaba.

Tsohon Gwamnan Oyo Olunloyo ya riga mu gidan gaskiya An yi wa wata mata ƙarin jini sau 36

“Mu dai muna kiwon akuya a wannan al’umma, amma ba ma cin namanta. Maimakon haka, muna sayar da su ne.

“A gaskiya, akwai doka a danginmu da ke hana kowa cin naman akuya cikin gidansa.

“Cin naman akuya wani abu ne da ba a yarda da shi ba a kauyenmu.

“Wannan al’ada ce da muka gada daga kakanninmu, kuma har yanzu muna kiyaye ta a cikin iyali.

“Wannan al’ada ta daɗe, ba mu ma san lokacin da ta fara a yankinmu ba.

“Mun tashi kawai muka ga iyayenmu suna yin hakan, mu kuma muka ci gaba,” in ji Muhammad.

Naman akuya na haifar da ƙuraje — masu cin naman

Jihar Sakkwato tana ɗaya daga cikin jihohin Arewacin Nijeriya da ke taka rawar gani wajen kiwon dabbobi.

Ana kiyasta cewa, jihar na da jimillar awaki miliyan 2.9 da shanu miliyan 3.4 da tumaki miliyan 1.9 da jakuna 40,000.

Sai dai duk da irin gudunmawar da jihar ke bayarwa wajen samar da dabbobi da kuma yadda mutanenta ke son cin nama, yawancin Fulani a Sakkwato ba sa cin naman akuya.

Jaridar Aminiya ta lura cewa, ba za a iya samun naman akuya da aka dafa ko aka soya a tukuba ko gidajen abinci da otal-otal a cikin babban birnin jihar ba.

Haka kuma ba kasafai ne mutanen Sakkwato ke yanka akuya a lokacin bukukuwan sallah ko suna ko bukukuwan aure ba.

Saboda wannan al’ada, yawancin awakin da ake samarwa a Sakkwato ana tura su ne zuwa Kudu maso Yamma da wasu makwabtan jihohi kamar Kano da Katsina da Kaduna domin a ci namansu a can.

A sakamakon haka, kadan daga cikin awakin da ake sarrafa su a cikin babban birnin jihar suna zuwa ne ga kabilun Yarbawa da Igbo da Egbira.

Tasirin wannan doguwar al’ada ya fi fitowa a cikin birane fiye da karkarar jihar Sakkwato.

Malam Ibrahim Auwal, wani mai sana’ar saye da sayar da dabbobi a kasuwar dabbobi ta Ƙofar Dundaye a Sakkwato, ya tabbatar da cewa, yawancin awakin da ake kawowa kasuwar ana tura su ne zuwa wasu jihohi don a siyar a can, yana mai cewa “mutanenmu nan Sakkwato ba sa cin naman akuya.”

“Fiye da kashi 90 cikin 100 na awakin da ake kawowa nan, ana tura su ne zuwa Kudu.

“Kashi 10 kawai ake sayarwa a cikin babban birnin jihar da kewaye.”

Da yake magana da wakilinmu ta wayar tarho, Alhaji Habibu Musa, wanda yake yanka dabbobi a kasuwar kara ta Sakkwato, ya bayyana cewa, saboda karancin cin naman akuya a Sakkwato, ana yanka awaki kadan ne a mayankarsu.

“A rana guda, ba mu yanka fiye da akuya 10 zuwa 15 ba saboda ba a cin naman akuya sosai a birnin Sakkwato.

“Duk da haka, Fulani da suke zaune a kauyuka kamar Bodinga da Gwadabawa da Illela da Dundaye da Dange da sauran kananan garuruwa suna cin naman akuya kuma ba su da wata matsala.

“Don haka, dan naman akuya da ake yankawa a nan yana zuwa wuraren nan don a ci.”

Wani mazaunin Sakkwato, Malam Bala Idris ya bayyana cewa, “a cikin iyalina, ba ma cin naman akuya, domin yana haifar mana da cutar fata, wadda muke kira Sameha wato ƙuraje a harshen Hausa.

“Ba wani daga iyalina da ke cin naman akuya. Haka muka tashi da wannan al’ada kuma muka ci gaba da ita. Matata da yara ma ba sa ci.”

Al’adar na ƙara raguwa

Wani babban jami’i a kafar yada labarai. wanda ya nemi a sakaya sunansa ya ce, yana sane da al’adun Fulani na kauce wa cin naman akuya, inda ya ce, “na san wannan al’adar, amma ina ganin tana raguwa a birane.

“Yawancin lokaci, akuya ana kallon ta a matsayin dabba mara kima idan aka kwatanta da saniya ko rago. Amma gaskiya al’adar tana canzawa.

“Ni kaina ina cin naman akuya. Ina ganin a birane mutane suna barin wadannan tsoffin al’adu na Fulani,” in ji shi.

Me ya sa ba a cin naman akuya?

Kabiru Zubairu, wani matashi Bafullatani da ke zaune a Dukku, Jihar Gombe, ya bayyana ra’ayinsa kan wannan al’ada ta kauce wa cin naman akuya.

Ya ce: “A ganina, akwai dalilai guda biyu da suka sa haka: na farko, an samo shi daga al’adar Fulani ta rashin cin naman akuya.

“Na biyu kuma, akwai wani tunani cewa, cin naman akuya na iya haifar da cuta, wadda ake kira saɗaure a harshen Fulfulde, wato yana kallon nama a matsayin mara kyau ga lafiya.

“Wannan tunanin har yanzu yana nan, yadda na sadaukar da akuya a lokacin babbar sallar na iya zama muhawara a tsakanin Fulani.

“Wannan yana nuna cewa, tunanin rashin cin naman akuya ya tsaya sosai.

“Amma idan akwai Fulani da ke ci yanzu, yana iya zama sakamakon tasirin zamansu a birane.”

Kabiru ya ƙara da cewa, wasu abubuwan zamantakewa, kamar auratayya tsakanin ƙabilu daban-daban, suna iya taimakawa wajen sassauta wannan al’ada.

Naman akuya ba ya cutar da lafiya

Sai dai Malam Salisu Maiwanki, wani Bafulatani daga Ƙaramar Hukumar Shira, Jihar Bauchi, yana cin naman akuya kuma ba ya cutar da shi.

Ya ce, “ni da iyalina, muna cin naman akuya kuma ba mu da wata matsala.

“A gaskiya, muna cin dukkan nau’o’in nama ba tare da fuskantar wata matsala ta lafiya ba.”

Dakta Lamaran Mansur, likita a Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano, ya bayyana cewa, wannan tunanin cewa naman akuya na cutarwa ba daidai ba ne a kimiyyance.

Ya ce, “wannan kawai tunani ne wanda ba a tabbatar da shi a kimiyyance ba a duniya.

“Naman akuya yana dauke da sinadarin protein mai yawa da kananan kitse, wanda ke da amfani sosai ga lafiya.”

Ya ƙara da cewa, idan gwamnati za ta ba da ilimi mai kyau kan wannan batu, za a iya cire wannan tunanin kuma mutane za su amfana da wannan nama mai albarka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Akuya Naman Akuya wa cin naman akuya a cin naman akuya awakin da ake wannan al ada Wannan al ada bayyana cewa a wannan al a Wannan al

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai

A cewar Bawa, gwamnatocin da a karkashinsu aka wawashe dukiyar kasa, su ne na Mulkin Tsohon Shugaban Kasa Olusegun Obasanjo (daga 1999 zuwa 2006), sai Marigayi Shugaba Umaru Musa Yar’Adua (daga 2007 zuwa 2009), kazalika a mulkin Shugaba Goodluck Jonathan daga (2010 zuwa 2014), sai kuma mulkin Muhammadu Buhari (daga 2015 zuwa 2023).

Wadannan bayanai na kunshe cikin littafin, ‘The Shadow Of Loot and Loss – Uncobering Nigeria’s Petrol Subsidy Fraud,’ wanda tsohon sarkin yaki da cin hanci da rashawa ya rubuta.

Alkaluman da Bawa ya bayyana daga cikin gwamnatocin hudu, shugaba Buhari ne ke kan gaba wajen biyan tallafin da ake ta cece-kuce akai na Naira tiriliyan 11, sai kuma na Jonathan wanda ya kashe Naira tiriliyan 3.9. Gwamnatin Obasanjo ta zo na uku da Naira biliyan 812 yayin da ‘Yar’aduwa ke biye da Naira biliyan 794.

Obasanjo da Buhari sun shafe shekaru takwas suna mulki yayin da Jonathan ya yi mulki na tsawon shekaru shida, tun da farko ya kammala shekaru biyu da gwamnatin Yar’adua ta bari, a matsayin mataimakin marigayin, inda ya lashe zaben shugaban kasa a shekarar 2011.

A cikin littafin mai shafuka 317, Bawa ya ce kudaden tallafin, wadanda galibi na yaudara ne, ana samun su ne ta hanyar rashin isassun tsare-tsare, raunin tsarin aiwatar da doka, da kuma rashin gaskiya a cikin dukkan tsarin.

Bawa ya ce wadannan kura-kurai sun karfafa karuwar kudaden tallafin daga Naira biliyan 123 a shekarar 2006 zuwa Naira biliyan 886 a shekarar 2014 da kuma mummunan adadi na Naira tiriliyan 11 a shekarar 2023.

Tsohon shugaban na EFCC ya ci gaba da cewa za’a iya bayyana badakalar tallafin man fetur ta Nijeriya ta hanyar amfani da triangle na zamba na “Tsarin (Needs), Opportunity and Rationalisation.”

Ya ce, “Matsi shi ne abin da zai sa mutum ya yi zamba, samun dama kuma ita ce ke bayar da yanayin da mutum zai aikata zambar.

 

Yadda Aka Aiwatar Da Badakalar

Bawa ya gano hauhawar farashin shigo da kayayyaki, da sauya lokacin daftarin kaya, rashin bayyana dawo da kayan da aka shigo da su ta sama da kasa, da jirgin ruwa mai yawo, shigo da kaya guda daya, tare da biyan tallafi a kansa sau biyu, na daga cikin hanyoyin da aka tafka badakalar tallafin man fetur.

A cewarsa, kamfanonin sayar da man sun yi amfani da yawan shigo da kayayyaki don kara yawan kudaden tallafi daga karshen shekarun 2010.

Ya ce binciken da aka gudanar ya sa hukumar EFCC ta gano haramtattun kudaden da suka haura Naira biliyan 30.

Bawa ya ci gaba da cewa, “A lokuta da dama, an samu jami’an gwamnati da saninsu ko kuma ba da saninsu ba, ta hanyar buga tambari da sanya hannu a cikin takardun jabun, wasu jami’an sun ce sun sanya hannu a kan takardun a lokacin da suke bakin aiki, duk da cewa suna sane da cewa lamarin ba haka yake ba, akwai wadanda suka sanya hannu kan takardun bogi, ba tare da sanin cewa an kirkiresu ba ne.

Ya ba da misali da yadda wani kamfani ya shigo da lita miliyan biyar kasa da mai fiye da lita miliyan 12. An biya kamfanin tallafin Naira miliyan 700, wanda bai cancanta ba.”

Wannan a cewarsa lamari ya ci gaba da haifar da tambayoyi masu mahimmanci game da hanyoyin damfara, gazawar sa ido na hukumomi, da kuma yadda EFCC ta gano wadannan haramtattun ayyuka.

 

Hanyar Kawo Karshen Lamarin

Dangane da kokarin hukumar na duba matsalar, Bawa ya ba da tarihin bincike, kamawa, tuhume-tuhume, yanke hukunci da kwato haramtattun dukiyoyi da hukumar ta yi.

Ya ce duk da cewa ba a samu wasu laifuka ba a shekarar 2006 da 2007, hukumar ta kwato Naira biliyan 11.5 a shekarar 2008, Naira biliyan 4.88 a shekarar 2009, da kuma Naira biliyan 10.3 a shekarar 2010.

Tsohon shugaban hukumar ta EFCC ya bayyana wata badakala da aka yi a 2011 ta tallafin man fetur, “a lokacin ne muka gano wasu haramtattum ayyukan da suka kai Naira biliyan 41.7.

“A dunkule, ayyukan damfara sun kai kusan Naira biliyan 68, wanda kusan kashi 80 cikin 100 an kwato su,” in ji shi.

Bawa ya kara da cewa, a cikin shekaru 25 na mulkin dimokuradiyya, Nijeriya ta kashe Naira tiriliyan 16.5 wajen bayar da tallafi, inda ya kara da cewa abin da ke daure kai ga daukacin al’amura shi ne yadda aka kashe kaso daga cikin kudaden wajen yin ikirarin karya da satar dukiyar kasa.

 

Hanyar Samun Ci Gaba

Bawa ya yi nuni da cewa, shi tallafin a kansa ba wani sharri ba ne; amma duk da haka, aiwatar da aikinta na yaudara ya sa gwamnati ta ki amincewa da dimbin albarkatun da aka tanada domin samar da ababen more rayuwa, inganta harkokin ilimi da kiwon lafiya, wadanda ke amfanar da marasa galihu a Nijeriya.

Don haka ya yi kira da a samar da ingantaccen tsarin bayar da tallafi.

Ya ce, “Kiyaye tsarin tallafin da aka sarrafa da kyau zai iya ba da agajin da ake bukata ga masu rauni ta hanyar tabbatar da cewa an dakatar da tsadar rayuwa, sannan gwamnatin ta tsaya tsayin daka wajen samar da wani abin dogaro ga matsalolin tattalin arziki.

“Wannan yana jaddada muhimmancin samar da ingantattun hanyoyin sa ido da daidaita yadda ake raba tallafin don hana cin zarafi da tabbatar da sun cika manufarsu.”

Bawa ya kuma yi kira da a ji tsoron Allah da gaske da kuma samar da ingantaccen tsarin adalci.

Bawa ya ce, “Tsarin ba wai kawai kayan ya ke ba wa kariya da kuma dakile laifuka ba, har ma ya mallakar karfin bincike da kuma hukunta laifukan da suka dace, yana da matukar muhimmanci, irin wannan tsarin na samar da amana da amincewa a tsakanin ‘yan kasa, tare da karfafa hadin gwiwar jama’a da kuma tabbatar da doka da oda.”

Tsohon shugaban na EFCC ya bukaci ‘yan Nijeriya da na kasashen waje da su canja halayensu, su bi ka’idojin da’a, su sanya al’ummar kasa a zuciyarsu sama da kansu.

Bugu da kari, ya yi kira da a samar da isassun kudade tare da tura fasahar kere-kere a cibiyoyin gwamnati domin dakile cin hanci da rashawa.

“Su koma al’adar yin abin da ya dace, ba tare da la’akari da yanayin ba, hakan na iya haifar da sauye-sauye masu dorewa a cikin al’amuran al’umma,” in ji shi.

LEADERSHIP Sunday ta ruwaito cewa an samu wasu ‘yan Nijeriya da dama da laifin zamba a cikin tallafin man fetur, na baya-bayan nan shi ne Mamman Ali, dan Ahmadu Ali, tsohon shugaban jam’iyyar PDP mai mulki a lokacin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Sanar Da Dakatar Da Tattaunawa Da Amurka A Wannan Lokaci Da Take Fuskantar Yaki Daga Isra’ila
  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
  • Kwamadan Sararin Samaniyar Iran Na Dakarun Kare Juyi Haji Zadeh Yana Cikin Wadanda Su Ka Yi Shahada
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai
  • Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan yankuna da dama na Iran ciki har da Tehran
  • Iran ta caccaki kudurin IAEA wanda ta ce yana cike da siyasa
  • Hamas : Ziyarar ministan Isra’ila Ben-Gvir a masallacin al-Aqsa kan iya tayar da yakin addini