Wasu Yan Siyasa A Burtaniya Suna Matsaya Gwamnatin Kasar Ta Amince Da Kasar Falasdinu
Published: 21st, May 2025 GMT
Kwamiti mai kula da al-amuran harkokin waje a kasar Burtaniya tana matsawa sakataren harkokin wajen kasar David Lammy kan cewa ya amince da kasar Falasdinu mai zaman Kanata.
Jaridar Telegram ta kasar Burtaniya ta nakalto wannan rahoton a yau Laraba, ta kuma kara da cewa Dan majalisa Emily Thomberrry ya kara da cewa wannan mataki na farko ne, idan Lammy ya bada wannan sanarwan a cikin wata mai zuwa a lokacin haduwarsa da Saudiya da Faransa a wani babban taro wanda zai bada damar daukar matakai nag aba.
Jaridar tace, wannan maganar tana zuwa ne bayan da sakataren ya dakatar da tattaunawa ta harkokin kasuwanci da HKI, da kuma kiran jakadan HKI a London don gabatar da korafinsa kan sake komawa yakin da gwamnatin HKI ta yi bayan an fara aiwatar da sulhun da aka amince da shi.
A babban zaben da ya gabata dai jam’iyyar Lebour ta ce zata amince da kasar Falasdinu mai cikeken yenci bisa fahintar samar da kasashe biyu. Amma benyamin natanyaho firai ministan HKI ya sha alwashin hana samuwar kasar Falasdinu kwata-kwata.
Yan majalisa ThornBerry ya fadawa Telegram kan cewa, a ra’ayinsa Burtaniya da Faransa sun amince da kafuwar kasar Falasdinu a taron Newyork wanda kasar Saudiya zata jagoranta a cikin watan Yuni mai zuwa.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Falasdinu
এছাড়াও পড়ুন:
An kai hari a ƙauyuka uku da kashe mutum 7 a Imo
A ranar Juma’a wasu ’yan bindiga sun kai hari wasu ƙauyuka uku na Umualoma da Ndiakunwanta da Ndiejezie a garin Arondizogu, a Ƙaramar hukumar Ideato ta Arewa a Jihar Imo, inda suka kashe aƙalla mutane bakwai.
An samu rahoton cewa, ’yan bindigar sun kai harin ne a kan babura sun yi ta harbin mutanen yankin a ƙauyukan Umualoma da Ndiakunwanta da Ndiejezie, inda suka kashe mutane da dama tare da jikkata wasu da dama.
An kashe mata da yara a sabon harin Filato Sarkin Katsinan Gusau ya rasuWaɗanda harin ya rutsa da su, masu shaguna ne da kwastomominsu da kuma masu wucewa.
Wata majiya da ta nemi a sakaya sunanta, ta shaida wa majiyarr PUNCH cewa, waɗanda lamarin ya rutsa da su na zaune ne a wuraren shan barasa, wasu kuma suna wasan diraf, a lokacin da ’yan bindigar da ke kan babur suka yi kamar suna wucewa, suka riƙa harbin kowa a wurin.
Majiyar ta ce, “Mutanen da suka mutu suna cikin mashaya daban-daban suna shaye-shaye, wasu kuma mutanen suna harkar kasuwanci da kula da kwastomominsu, sai aka ji ƙarar harbin mutanen da suke zaune a lokacin, kamar yadda nake magana da ku, kusan mutane 12 ne ke kwance ake tsammanin sun mutu, wasu da dama kuma sun samu munanan raunuka saboda gudun neman tsira.
Da yake tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a, kakakin rundunar ’yan sandan jihar, Henry Okoye ya ce mutane bakwai ne suka mutu sannan wasu da dama suka jikkata.
Okoye ya ci gaba da cewa, al’amura sun dawo daidai kamar yadda aka saba a ƙauyukan yayin da aka baza jami’an tsaro tare da gudanar da bincike mai zurfi domin gano waɗanda suka aikata kisan.