Jagoran juyin juya halin Musulunci ya jaddada cewa: Ba su tunanin cewa tattaunawar Iran da Amurka za ta haifar da kyakkyawan sakamako

Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya bayyana cewa: Iran ba ta jiran izinin kowa wajen inganta sinadarin Uranium, kuma Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana da manufofinta.

Jagoran ya ce ba su yarda cewa tattaunawar za ta kai ga cimma nasara ba.

A jiya Talata ne aka gudanar da biki a Husainiyar Imam Khumaini (r.a) na tunawa da shahadar marigayi shugaban kasa Ayatullah Ibrahim Raisi da mukarrabansa. Bikin ya samu halartar Jagoran juyin juya halin Musulunci, da shugabannin bangarori uku na gwamnati, da manyan jami’ai, da taron iyalan shahidai, da kuma bangarori daban-daban na al’umma.

Jagoran juyin juya halin Musulunci ya bayyana a wajen wannan biki cewa: Shahidi Ra’isi bai dauki kansa a matsayin wanda ya fi mutane ba; Ya dauki kansa a matsayi daya daga cikin jama’a, kamar sauran jama’a, har ma kasancewarsa karami fiye da sauran mutane.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Jagoran juyin juya halin Musulunci

এছাড়াও পড়ুন:

Tattaunawar Iran da Amurka na inganta zaman lafiya a yankin : Araghchi

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya bayyana cewa, tattaunawar dake tsakanin Iran da Amurka za ta iya taka rawar gani wajen samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

A yayin da yake zantawa da manema labarai a gefen dandalin tattaunawa na Tehran, Araghchi ya ce kasashen yankin suna goyon bayan tattaunawar da ake yi tsakanin Iran da Amurka.

” Zaman lafiya da kwanciyar hankali su ne batutuwa mafi muhimmanci ga dukkan kasashen yankin,” in ji shi.

Ya nanata matsayar Iran kan turbar diflomasiyya da kuma muhimmancin da take baiwa manufofin kyakkyawar makobtaka ta hanyar tattaunawa.

A wani bangare na jawabin nasa, ministan harkokin wajen na Iran ya ce dandalin tattaunawa na Tehran karo na shida ya samu halartar masana da jami’an kasashen waje da ba a taba ganin irinsa ba.

Wannan yunkuri a cewarsa, ya bayyana yuwuwar Teheran a matsayin cibiyar musayar ra’ayi kan batutuwan da suka shafi shiyya-shiyya da na ƙasa da ƙasa.

Bugu da kari, ministan harkokin wajen na Iran ya ce ya tattauna da takwarorinsa na Oman da Qatar kan tattaunawa da Amurka.

Mista Araghchi ya yi maraba da matakin da kasashen yankin musamman na yankin tekun Fasha suka dauka na sauya ra’ayinsu game da Iran, kamar yadda suke a matsayin “kyau” dangane da shawarwarin da aka yi tsakanin Tehran da Washington.

Idan dai ba a manta ba a farkon watan Afrilu ne aka fara tattaunawa tsakanin Iran da Amurka karkashin jagorancin masarautar Oman.

Ya zuwa yanzu dai an gudanar da shawarwari guda hudu kan shirin nukiliyar Teheran da kuma dage takunkumin. Bangarorin biyu duk sun bayyana tattaunawar a matsayin mai kyau da kuma amfani.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sharhin Bayan Labarai: Iran Zata Ci Gaba Da Tashe Uranium Tare Da Yarjeniya Ko Babu Ita
  • Wulayati Ya Ce Samun Kalamai Masu Karo Da Juna Tsakanin Trump Da Mukarrabansa Yana Zubar Da Kwarin Gwiwa
  • Jagora: Jamhuriyar Musulunci Ba Ta Bukatar Izinin Wani Mahaluki Domin Tace Sanadarin Uranium
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ta Iran Ya Ce: Haramtacciyar Kasar Isra’ila Ba Ta Da Alkiblar Siyasa
  • Tattaunawar Iran da Amurka na inganta zaman lafiya a yankin : Araghchi
  • Trump ya ce ya yi tattaunawa mai armashi da Putin
  • Iran Ta Ce Gabatar Da Bukatar Dakatar Da Tashe Makamashin Uranium Karshen Tattaunawar Da Amurka
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Fatan Tattaunawar Kasarsa Da Amurka Ta Cimma Yarjejeniya Ta Gaskiya
  • Iran : zamu ci gaba da inganta uranium ko da yarjejeniya ko babu